• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Soja Da Wasu 24 A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Taraba

by Sadiq
3 years ago
Taraba

An yi wa wani jami’in soja kwanton bauna tare da wasu mutanen 24 mazauna kananan hukumomin Ussa da Takum a Jihar Taraba.

A cewar kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Taraba, Abdullahi Usman, mutane 24 ne suka mutu.

  • Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da Ukraine Ta Nuna Yadda Sin Ta Sauke Nauyi Dake Wuyanta
  • Da Dumi-Dumi: NEC Ta Dakatar Da Cire Tallafin Man Fetur

“Jami’in sojan da ya fito daga shingen binciken da ke dawowa barikin bataliya ta 93 an yi masa kwanton bauna aka kashe shi, duk da cewa ba a kwace masa babur dinsa ba, kuma aka yi sa’a ba shi da bindiga a tare da shi.

“Wadanda ba a san ko su wane ne ba ne suka kashe shi, kuma an fara bincike don bankado wadanda suka aikata kisan. Bisa kididdigar da aka yi, an kashe ‘yan asalin kabilar Kuteb 20 yayin da wasu Fulani makiyaya uku kuma suka mutu a sakamakon rikicin,” in ji kakakin.

Ya kara da cewa babbar matsalar da ta dakile dawo da zaman lafiya a yankin, ita ce ikirarin da Fulani makiyaya suka yi na cewa manoman Kuteb sun yi garkuwa da shanunsu da kuma hana wasu bangarorin da suka kasa shiga gonakinsu saboda fargabar da ake yi musu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

“Matsalar da muke fuskanta a halin yanzu ita ce, Fulani na ikirarin cewa an sace musu shanu kuma ana garkuwa da su a yankunan manoman Kuteb yayin da ‘yan Kuteb ke fargabar zuwa gona saboda fargabar harin Fulani makiyaya.

“Kwamishanan ‘yan sanda ya yi kira ga shugaban kungiyar makiyaya ta Miyetti Allah da ke Ussa da su yi kokarin wanzar da zaman lafiya a yankin,” in ji shi.

Shugaban kungiyar Kuteb Yatgso ta Nijeriya, Emmanuel Ukwen, ya ce a matsayinsa na shugaban al’ummarsa bai ga gwamnatin jihar ta ziyarci mutanensa ba ko ta tausaya musu ba.

Sannan ya musanta sama wa jama’arsa matsuguni sakamakon rikicin da ya yi sanadin raba wasu da muhallansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Manyan Bankunan Zuba Jari Na Duniya Sun Daga Hasashen Ci Gaban GDPn Sin Zuwa Kaso 6% Ko Fiye

Manyan Bankunan Zuba Jari Na Duniya Sun Daga Hasashen Ci Gaban GDPn Sin Zuwa Kaso 6% Ko Fiye

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.