ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Soja Da Wasu 24 A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Taraba

by Sadiq
3 years ago
Taraba

An yi wa wani jami’in soja kwanton bauna tare da wasu mutanen 24 mazauna kananan hukumomin Ussa da Takum a Jihar Taraba.

A cewar kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Taraba, Abdullahi Usman, mutane 24 ne suka mutu.

  • Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da Ukraine Ta Nuna Yadda Sin Ta Sauke Nauyi Dake Wuyanta
  • Da Dumi-Dumi: NEC Ta Dakatar Da Cire Tallafin Man Fetur

“Jami’in sojan da ya fito daga shingen binciken da ke dawowa barikin bataliya ta 93 an yi masa kwanton bauna aka kashe shi, duk da cewa ba a kwace masa babur dinsa ba, kuma aka yi sa’a ba shi da bindiga a tare da shi.

ADVERTISEMENT

“Wadanda ba a san ko su wane ne ba ne suka kashe shi, kuma an fara bincike don bankado wadanda suka aikata kisan. Bisa kididdigar da aka yi, an kashe ‘yan asalin kabilar Kuteb 20 yayin da wasu Fulani makiyaya uku kuma suka mutu a sakamakon rikicin,” in ji kakakin.

Ya kara da cewa babbar matsalar da ta dakile dawo da zaman lafiya a yankin, ita ce ikirarin da Fulani makiyaya suka yi na cewa manoman Kuteb sun yi garkuwa da shanunsu da kuma hana wasu bangarorin da suka kasa shiga gonakinsu saboda fargabar da ake yi musu.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

“Matsalar da muke fuskanta a halin yanzu ita ce, Fulani na ikirarin cewa an sace musu shanu kuma ana garkuwa da su a yankunan manoman Kuteb yayin da ‘yan Kuteb ke fargabar zuwa gona saboda fargabar harin Fulani makiyaya.

“Kwamishanan ‘yan sanda ya yi kira ga shugaban kungiyar makiyaya ta Miyetti Allah da ke Ussa da su yi kokarin wanzar da zaman lafiya a yankin,” in ji shi.

Shugaban kungiyar Kuteb Yatgso ta Nijeriya, Emmanuel Ukwen, ya ce a matsayinsa na shugaban al’ummarsa bai ga gwamnatin jihar ta ziyarci mutanensa ba ko ta tausaya musu ba.

Sannan ya musanta sama wa jama’arsa matsuguni sakamakon rikicin da ya yi sanadin raba wasu da muhallansu.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Manyan Bankunan Zuba Jari Na Duniya Sun Daga Hasashen Ci Gaban GDPn Sin Zuwa Kaso 6% Ko Fiye

Manyan Bankunan Zuba Jari Na Duniya Sun Daga Hasashen Ci Gaban GDPn Sin Zuwa Kaso 6% Ko Fiye

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.