ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Soja Da Wasu 24 A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Taraba

by Sadiq
3 years ago
Taraba

An yi wa wani jami’in soja kwanton bauna tare da wasu mutanen 24 mazauna kananan hukumomin Ussa da Takum a Jihar Taraba.

A cewar kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Taraba, Abdullahi Usman, mutane 24 ne suka mutu.

  • Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da Ukraine Ta Nuna Yadda Sin Ta Sauke Nauyi Dake Wuyanta
  • Da Dumi-Dumi: NEC Ta Dakatar Da Cire Tallafin Man Fetur

“Jami’in sojan da ya fito daga shingen binciken da ke dawowa barikin bataliya ta 93 an yi masa kwanton bauna aka kashe shi, duk da cewa ba a kwace masa babur dinsa ba, kuma aka yi sa’a ba shi da bindiga a tare da shi.

ADVERTISEMENT

“Wadanda ba a san ko su wane ne ba ne suka kashe shi, kuma an fara bincike don bankado wadanda suka aikata kisan. Bisa kididdigar da aka yi, an kashe ‘yan asalin kabilar Kuteb 20 yayin da wasu Fulani makiyaya uku kuma suka mutu a sakamakon rikicin,” in ji kakakin.

Ya kara da cewa babbar matsalar da ta dakile dawo da zaman lafiya a yankin, ita ce ikirarin da Fulani makiyaya suka yi na cewa manoman Kuteb sun yi garkuwa da shanunsu da kuma hana wasu bangarorin da suka kasa shiga gonakinsu saboda fargabar da ake yi musu.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

“Matsalar da muke fuskanta a halin yanzu ita ce, Fulani na ikirarin cewa an sace musu shanu kuma ana garkuwa da su a yankunan manoman Kuteb yayin da ‘yan Kuteb ke fargabar zuwa gona saboda fargabar harin Fulani makiyaya.

“Kwamishanan ‘yan sanda ya yi kira ga shugaban kungiyar makiyaya ta Miyetti Allah da ke Ussa da su yi kokarin wanzar da zaman lafiya a yankin,” in ji shi.

Shugaban kungiyar Kuteb Yatgso ta Nijeriya, Emmanuel Ukwen, ya ce a matsayinsa na shugaban al’ummarsa bai ga gwamnatin jihar ta ziyarci mutanensa ba ko ta tausaya musu ba.

Sannan ya musanta sama wa jama’arsa matsuguni sakamakon rikicin da ya yi sanadin raba wasu da muhallansu.

MASU ALAKA

Taraba
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Taraba
Manyan Labarai

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
Manyan Labarai

Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya

July 24, 2026
Next Post
Manyan Bankunan Zuba Jari Na Duniya Sun Daga Hasashen Ci Gaban GDPn Sin Zuwa Kaso 6% Ko Fiye

Manyan Bankunan Zuba Jari Na Duniya Sun Daga Hasashen Ci Gaban GDPn Sin Zuwa Kaso 6% Ko Fiye

LABARAI MASU NASABA

Taraba

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

July 25, 2026
Taraba

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Taraba

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
Taraba

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.