• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Bindiga 4 Da Cafke Matar Da Ke Kai Wa ‘Yan Ta’adda Makamai A Kaduna

byKhalid Idris Doya
3 years ago
An

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ta ce, jami’anta sun samu nasarar hallaka ‘yan bindiga guda hudu (4) a musayar wuta da suka yi da su da kama wata mata da take musu safarar bindigogi da alburusai a jihar Kaduna.

Kamar yadda jami’in hulda da jama’a na hukumar reshen jihar Kaduna, DSP Muhammed Jalige, ya shaida ta cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Mutan 3 Yankan Rago Da Sace Wasu Da Dama A Wani Sabon Hari A Neja
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutun 3, Sun Sace 30 A Jihar Neja

Jalige ya ce, nasarar ta biyo bayan kokarin jami’an ‘yan sanda na STS da hadin guiwar sojojin Operation Yaki suka samu wurin kawo karshen ayyukan ‘yan bindiga, inda a ranar 15 ga watan Yuni suka cafke wadanda ake zargin ‘yan bindiga ne a kan hanyar Saminaka zuwa Jos.

Ya ce, an kama ‘yan bindigan ne a cikin wata mota kirar Sharon mai launin bulu tare da matukinta mai suna James Dawi Dan shekara 31 a duniya mazaunin yankin Vom da ke Kudancin jihar Filato.

Ya kara da cewa a wannan yanayin da suka tabbatar ba za su iya tsallake tarkon jami’an tsaron ba gami da kokarinsu na kai bindigogi ga abokan cin burminsu, nan take suka bude ruwan harsasai ga jami’an tsaron.

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Jami’in yada labaran ya ci gaba da cewa, cikin dabarun na aiki da kwarewa, jami’an tsaron sun samu nasarar harbin hudu daga cikin ‘yan bindigan kana an kwashesu zuwa asibitin koyarwa ta Barau Dikko da ke Kaduna inda likita ya tabbatar da mutuwarsu.

Ya ce, sun samu nasarar kwato wasu makamai daga wajen ‘yan bindigan bayan da aka sha karfinsu, “A yayin artabun an kama wata mace da ake bincikenta ta tabbatar da kanta cewa tana safaran bindigogi da alburusai ga ‘yan bindiga a yankin Kaduna.”

Ya ce, bincike dai na cigaba da gudana domin dakile aniyar bata-garin da suka addabi Kaduna da garkuwa da mutane da fashi da makami.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Next Post
SEMA Ta Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira Kayan Abinci A Jihar Borno

SEMA Ta Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira Kayan Abinci A Jihar Borno

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version