ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Bindiga 4 Da Cafke Matar Da Ke Kai Wa ‘Yan Ta’adda Makamai A Kaduna

by Khalid Idris Doya
3 years ago
An

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ta ce, jami’anta sun samu nasarar hallaka ‘yan bindiga guda hudu (4) a musayar wuta da suka yi da su da kama wata mata da take musu safarar bindigogi da alburusai a jihar Kaduna.

Kamar yadda jami’in hulda da jama’a na hukumar reshen jihar Kaduna, DSP Muhammed Jalige, ya shaida ta cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Mutan 3 Yankan Rago Da Sace Wasu Da Dama A Wani Sabon Hari A Neja
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutun 3, Sun Sace 30 A Jihar Neja

Jalige ya ce, nasarar ta biyo bayan kokarin jami’an ‘yan sanda na STS da hadin guiwar sojojin Operation Yaki suka samu wurin kawo karshen ayyukan ‘yan bindiga, inda a ranar 15 ga watan Yuni suka cafke wadanda ake zargin ‘yan bindiga ne a kan hanyar Saminaka zuwa Jos.

ADVERTISEMENT

Ya ce, an kama ‘yan bindigan ne a cikin wata mota kirar Sharon mai launin bulu tare da matukinta mai suna James Dawi Dan shekara 31 a duniya mazaunin yankin Vom da ke Kudancin jihar Filato.

Ya kara da cewa a wannan yanayin da suka tabbatar ba za su iya tsallake tarkon jami’an tsaron ba gami da kokarinsu na kai bindigogi ga abokan cin burminsu, nan take suka bude ruwan harsasai ga jami’an tsaron.

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

Jami’in yada labaran ya ci gaba da cewa, cikin dabarun na aiki da kwarewa, jami’an tsaron sun samu nasarar harbin hudu daga cikin ‘yan bindigan kana an kwashesu zuwa asibitin koyarwa ta Barau Dikko da ke Kaduna inda likita ya tabbatar da mutuwarsu.

Ya ce, sun samu nasarar kwato wasu makamai daga wajen ‘yan bindigan bayan da aka sha karfinsu, “A yayin artabun an kama wata mace da ake bincikenta ta tabbatar da kanta cewa tana safaran bindigogi da alburusai ga ‘yan bindiga a yankin Kaduna.”

Ya ce, bincike dai na cigaba da gudana domin dakile aniyar bata-garin da suka addabi Kaduna da garkuwa da mutane da fashi da makami.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
Al'ajabi

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
Next Post
SEMA Ta Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira Kayan Abinci A Jihar Borno

SEMA Ta Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira Kayan Abinci A Jihar Borno

LABARAI MASU NASABA

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025
Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.