• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Bindiga Da Cafke 19 A Filato Da Kaduna

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Sojoji

Dakarun da ke aiki da rundunar ‘Operation SAFE HAVEN’ (OPSH) sun kashe ‘yan bindiga hudu tare da cafke akalla mutum 19 da ake zargi da suka hada da masu garkuwa da mutum da barayin shanu da kuma ‘yan fashi da makami a wani samame da suka kai maboyar ‘yan ta’adda a Jihohin Filato da Kaduna.

Rundunar sojin Nijeriya ta bayyana hakan ne a shafinta na Twitter (D).

  • Dino Melaye Ya Lashe Akwatin Zabensa A Kogi
  • Gwamnonin PDP Sun Karyata Shirin Mubaya’a Ga Tinubu

“An kama mutum 19 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban. An kama uku da laifin yin garkuwa da wani mutum yayin da aka kama hudu da laifin kisan kai.

An kama mutum hudu da ake zargi da kai hare-hare a kauyuka, biyu kuma da laifin safarar miyagun kwayoyi, yayin da aka kashe ‘yan bindiga hudu. Har ila yau, an kubutar da mutum hudu daga hannun masu garkuwa, yayin da aka dakile hare-hare shida kan al’ummomin da ba su da karfi, sannan an amsa kiran gaggawa 13,” in ji sanarwar a wani bangare.

A ranar 29 ga Oktoba, 2023, sojojin sun kama wasu da ake zargin dillalan miyagun kwayoyi ne, Mista Obinna Nwafor da Fatai Lawal a Kasuwar Kujiya Bukuru a Karamar Hukumar Jos ta Kudu, Jihar Filato, inda suka kwato wata bindiga kirar gida.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Washegari jami’an OPSH na Sector 7 sun kama wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne, Bawa Ahmad a Kauyen Kamuru da ke Karamar Hukumar Zango Kataf a Jihar Kaduna tare da kwato bindiga guda daya ta gida da kuma harsashi.

“A ranar 30 ga Oktoba, 2023, bisa ga sahihin labari, sojoji sun kama wasu mutum uku, Ibrahim Mohammed, Salisu Abdullahi da Idris Abdullahi da hada baki a harin da aka kai wa manoma a Kauyen Mai Hakorin Gold da ke Karamar Hukumar Bokkos, Jihar Filato.

“Hakazalika, sojoji sun kama wasu mutum uku, Dabid Emmanuel, Moses Dalyop da Gabriel Dabou, da hadin baki a kisan wani direban babur mai suna Abdulkarim Saidu, a Kauyen Shonong dake Karamar Hukumar Riyom, Jihar Filato.

“An kama wadanda ake zargin ne a kauyen Fang da ke Karamar Hukumar Riyom a ranar 30 ga Oktoba 2023. Wadanda ake zargin sun jagoranci sojoji wajen nemo gawar direban babur da aka kashe. A wannan rana, sojoji sun ceto wata Mis Abigail Felid da aka yi garkuwa da su a ranar 28 ga Oktoba, 2023, a Kauyen Angwan Malam da ke Karamar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna. Tuni dai matar da aka yi garkuwar da ita aka sake hada ta da danginta,” in ji sanarwar.

A ranar 1 ga Nuwamba, an kama wasu mutum biyu da ake zargi da satar babura Samaila Nasiru, Bashir Sani a babban yankin Riyom na Jihar Filato. Sojojin tare da hadin gwiwar Cibilian Joint Task Force sun kuma ceto wasu mutum biyu da aka yi garkuwa da su a unguwar Zobolo da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Harbe Barawon Akwatin Zabe A Kogi

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

Ƴansanda Sun Kama Gungun Masu Sojan Gona Suna Aikata Laifuka A Kano

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.