• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Bindiga Da Cafke 19 A Filato Da Kaduna

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Sojoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dakarun da ke aiki da rundunar ‘Operation SAFE HAVEN’ (OPSH) sun kashe ‘yan bindiga hudu tare da cafke akalla mutum 19 da ake zargi da suka hada da masu garkuwa da mutum da barayin shanu da kuma ‘yan fashi da makami a wani samame da suka kai maboyar ‘yan ta’adda a Jihohin Filato da Kaduna.

Rundunar sojin Nijeriya ta bayyana hakan ne a shafinta na Twitter (D).

  • Dino Melaye Ya Lashe Akwatin Zabensa A Kogi
  • Gwamnonin PDP Sun Karyata Shirin Mubaya’a Ga Tinubu

“An kama mutum 19 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban. An kama uku da laifin yin garkuwa da wani mutum yayin da aka kama hudu da laifin kisan kai.

An kama mutum hudu da ake zargi da kai hare-hare a kauyuka, biyu kuma da laifin safarar miyagun kwayoyi, yayin da aka kashe ‘yan bindiga hudu. Har ila yau, an kubutar da mutum hudu daga hannun masu garkuwa, yayin da aka dakile hare-hare shida kan al’ummomin da ba su da karfi, sannan an amsa kiran gaggawa 13,” in ji sanarwar a wani bangare.

A ranar 29 ga Oktoba, 2023, sojojin sun kama wasu da ake zargin dillalan miyagun kwayoyi ne, Mista Obinna Nwafor da Fatai Lawal a Kasuwar Kujiya Bukuru a Karamar Hukumar Jos ta Kudu, Jihar Filato, inda suka kwato wata bindiga kirar gida.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Washegari jami’an OPSH na Sector 7 sun kama wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne, Bawa Ahmad a Kauyen Kamuru da ke Karamar Hukumar Zango Kataf a Jihar Kaduna tare da kwato bindiga guda daya ta gida da kuma harsashi.

“A ranar 30 ga Oktoba, 2023, bisa ga sahihin labari, sojoji sun kama wasu mutum uku, Ibrahim Mohammed, Salisu Abdullahi da Idris Abdullahi da hada baki a harin da aka kai wa manoma a Kauyen Mai Hakorin Gold da ke Karamar Hukumar Bokkos, Jihar Filato.

“Hakazalika, sojoji sun kama wasu mutum uku, Dabid Emmanuel, Moses Dalyop da Gabriel Dabou, da hadin baki a kisan wani direban babur mai suna Abdulkarim Saidu, a Kauyen Shonong dake Karamar Hukumar Riyom, Jihar Filato.

“An kama wadanda ake zargin ne a kauyen Fang da ke Karamar Hukumar Riyom a ranar 30 ga Oktoba 2023. Wadanda ake zargin sun jagoranci sojoji wajen nemo gawar direban babur da aka kashe. A wannan rana, sojoji sun ceto wata Mis Abigail Felid da aka yi garkuwa da su a ranar 28 ga Oktoba, 2023, a Kauyen Angwan Malam da ke Karamar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna. Tuni dai matar da aka yi garkuwar da ita aka sake hada ta da danginta,” in ji sanarwar.

A ranar 1 ga Nuwamba, an kama wasu mutum biyu da ake zargi da satar babura Samaila Nasiru, Bashir Sani a babban yankin Riyom na Jihar Filato. Sojojin tare da hadin gwiwar Cibilian Joint Task Force sun kuma ceto wasu mutum biyu da aka yi garkuwa da su a unguwar Zobolo da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kudancin KadunaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitul Malin Amurka

Next Post

An Harbe Barawon Akwatin Zabe A Kogi

Related

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

2 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

3 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

4 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

7 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

8 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

9 hours ago
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Harbe Barawon Akwatin Zabe A Kogi

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.