• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe ‘Yan Bindiga Da Cafke 19 A Filato Da Kaduna

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Sojoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dakarun da ke aiki da rundunar ‘Operation SAFE HAVEN’ (OPSH) sun kashe ‘yan bindiga hudu tare da cafke akalla mutum 19 da ake zargi da suka hada da masu garkuwa da mutum da barayin shanu da kuma ‘yan fashi da makami a wani samame da suka kai maboyar ‘yan ta’adda a Jihohin Filato da Kaduna.

Rundunar sojin Nijeriya ta bayyana hakan ne a shafinta na Twitter (D).

  • Dino Melaye Ya Lashe Akwatin Zabensa A Kogi
  • Gwamnonin PDP Sun Karyata Shirin Mubaya’a Ga Tinubu

“An kama mutum 19 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban. An kama uku da laifin yin garkuwa da wani mutum yayin da aka kama hudu da laifin kisan kai.

An kama mutum hudu da ake zargi da kai hare-hare a kauyuka, biyu kuma da laifin safarar miyagun kwayoyi, yayin da aka kashe ‘yan bindiga hudu. Har ila yau, an kubutar da mutum hudu daga hannun masu garkuwa, yayin da aka dakile hare-hare shida kan al’ummomin da ba su da karfi, sannan an amsa kiran gaggawa 13,” in ji sanarwar a wani bangare.

A ranar 29 ga Oktoba, 2023, sojojin sun kama wasu da ake zargin dillalan miyagun kwayoyi ne, Mista Obinna Nwafor da Fatai Lawal a Kasuwar Kujiya Bukuru a Karamar Hukumar Jos ta Kudu, Jihar Filato, inda suka kwato wata bindiga kirar gida.

Labarai Masu Nasaba

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Washegari jami’an OPSH na Sector 7 sun kama wani da ake zargin mai garkuwa da mutane ne, Bawa Ahmad a Kauyen Kamuru da ke Karamar Hukumar Zango Kataf a Jihar Kaduna tare da kwato bindiga guda daya ta gida da kuma harsashi.

“A ranar 30 ga Oktoba, 2023, bisa ga sahihin labari, sojoji sun kama wasu mutum uku, Ibrahim Mohammed, Salisu Abdullahi da Idris Abdullahi da hada baki a harin da aka kai wa manoma a Kauyen Mai Hakorin Gold da ke Karamar Hukumar Bokkos, Jihar Filato.

“Hakazalika, sojoji sun kama wasu mutum uku, Dabid Emmanuel, Moses Dalyop da Gabriel Dabou, da hadin baki a kisan wani direban babur mai suna Abdulkarim Saidu, a Kauyen Shonong dake Karamar Hukumar Riyom, Jihar Filato.

“An kama wadanda ake zargin ne a kauyen Fang da ke Karamar Hukumar Riyom a ranar 30 ga Oktoba 2023. Wadanda ake zargin sun jagoranci sojoji wajen nemo gawar direban babur da aka kashe. A wannan rana, sojoji sun ceto wata Mis Abigail Felid da aka yi garkuwa da su a ranar 28 ga Oktoba, 2023, a Kauyen Angwan Malam da ke Karamar Hukumar Sanga ta Jihar Kaduna. Tuni dai matar da aka yi garkuwar da ita aka sake hada ta da danginta,” in ji sanarwar.

A ranar 1 ga Nuwamba, an kama wasu mutum biyu da ake zargi da satar babura Samaila Nasiru, Bashir Sani a babban yankin Riyom na Jihar Filato. Sojojin tare da hadin gwiwar Cibilian Joint Task Force sun kuma ceto wasu mutum biyu da aka yi garkuwa da su a unguwar Zobolo da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kudancin KadunaYan bindigaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Sakatariyar Baitul Malin Amurka

Next Post

An Harbe Barawon Akwatin Zabe A Kogi

Related

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

2 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

3 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

5 hours ago
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

8 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

9 hours ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

11 hours ago
Next Post
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Harbe Barawon Akwatin Zabe A Kogi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.