Hedikwatar tsaro ta bayyana cewa an kashe ‘yan ta’adda 6,260 a fadin kasar ta hanyar aikin hadin gwiwa na sojojin kasar a cikin shekaru biyu da suka gabata.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da sojojin suka kuma kwato danyen mai da wanda aka sarrafa da aka kiyasta darajarsa ta kai sama da Naira biliyan 83 a cikin wannan lokaci.
- Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
- Masarautar Gaya Ta Ƙwace Sarautar Wazirin Gaya Da Ta Bai Wa Tsohon Sakataren Gwamnatin Kano
Mataimakin Darakta mai kula da harkokin yada labarai na tsaro, Brig.-Gen. Ibrahim Abu-Mawashi ya bayyana hakan a lokacin da yake bayani kan nasarorin da sojojin suka samu a cikin shekaru biyu a wani taro na manema labarai a hedikwatar tsaro, ranar Alhamis.
Brig.-Gen. Abu-Mawashi ya kara da cewa an kama ‘yan ta’adda 14,138 da sauran masu aikata laifuka yayin da aka ceto mutane 5,365 a cikin wannan lokaci.
Abu-Mawashi ya ci gaba da cewa, sojojin sun kwato daruruwan makamai da kuma harsashi da yawa duk acikin wannan lokaci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp