• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

by Sulaiman
3 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sake haduwa da takwarorinsa na kasashen Kazakhstan da Kyrgyzstan da Tajikistan da Turkmenistan da kuma Uzbekistan a birnin Astana, inda suka halarci taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na biyu, don bude sabon babin hadin gwiwar kasashensu. 

Haduwarsu a wannan karo ta biyo bayan wacce suka yi a yayin taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na farko da aka gudanar a birnin Xi’an na kasar Sin shekaru biyu da suka wuce. A wannan karo kuma, kasashen sun fitar da sanarwar Astana game da taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na biyu, tare da rattaba hannu a kan yarjejeniyar kyakkyawar makwabtaka da abota da kuma hadin gwiwa na dindindin, baya ga shirye-shiryen hadin gwiwa har 110 da suka cimma.

  • IGP Ya Sake Bayar Da Umarnin Cafko Masa Mai Magana Da Yawun Gwamnan Kano Kan Bata Wa Ganduje 
  • Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

Sai dai ma’anar taron ba ta tsaya ga wadannan nasarorin da aka cimma ba, abun da ya fi muhimmanci shi ne taron ya shaida inda za mu dosa musamman a yayin da duniyarmu ke fama da rashin tabbas da tashe-tashen hankula.

A yayin da shugaba Xi Jinping ke halartar taron, ya gabatar da jawabi, inda ya bayyana hadin gwiwar Sin da kasashen tsakiyar Asiya a matsayin “ruhin Sin da kasashen tsakiyar Asiya”, da ke “martaba juna da amincewa da juna da cin moriyar juna da kuma taimakon juna, da zamanantar da kowa ta tabbatar da ci gaba mai inganci.”

A bisa ruhin ne, Sin da kasashen nan biyar ke ta fadada hadin gwiwarsu, tare da karfafa hadin kansu don rungumar kyakkyawar makomarsu ta bai-daya. Idan mun duba, tun bayan taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya karo na farko da aka gudanar a shekaru biyu da suka wuce, adadin cinikin da ke tsakanin Sin da kasashen nan biyar ya karu da kaso 35%, baya ga yadda suka inganta hadin gwiwarsu ta fannonin zuba jari da hakar ma’adinai ba tare da gurbata muhalli ba, da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha. Baya ga haka, a hukumance ne aka fara aikin gina layin dogon da ya ratsa kasashen Sin da Kyrgyzstan da Uzbekistan, kuma Sin da kasashen sun gina cibiyoyin al’adu a kasashen juna, kana Sin da Kazakhstan da kuma Uzbekistan sun cire wa al’ummomin juna bizar shiga kasashensu.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

A shekaru biyu da suka wuce, shugaban kasar Sin da takwarorinsa na kasashen nan biyar sun dasa wasu bishiyoyin ruman guda shida a birnin Xi’an, wadanda yanzu haka cike suke da furanni tare da alamanta hadin gwiwar kasashen mai cike da kyawawan nasarori, wadanda kuma suka shaida cewa, “hannu daya ba ya daukar jinka”, hada karfi da karfe ne zai kai ga inda aka dosa, kuma ba wanda ke iya cin nasara daga faduwar wasu, kuma za a iya tabbatar da nasara ga juna ne kurum idan aka zama tsintsiya madaurinki guda.

Yanzu haka, duniyarmu na fama da rikice-rikice da kariyar ciniki da ra’ayi na kashin kai da kuma siyasar nuna fin karfi. Amma bai kamata a mai da hannun agogon baya ba, kuma ba za a yarda da rarrabuwar kawuna a tsakanin al’ummomin duniya ba, kana ‘yan Adam bai kamata su koma irin rayuwar da masu karfi ke cin zalin masu karamin karfi kamar yadda aka yi a baya ba.

Daga birnin Xi’an zuwa Astana, Sin da kasashen tsakiyar Asiya sun samar da ruhin da ya amsa tambayar da zamaninmu ya aza mana, wato “me ya faru a duniyarmu, kuma me ya kamata mu yi”, wanda kuma ya karfafa mana niyyar kiyaye adalci da cin moriyar juna da samun nasara tare, don kiyaye zaman lafiyar duniya da tabbatar da ci gaban kasa da kasa baki daya. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Gurfanar Da Natasha A Kotu Kan Zargin Ɓata Sunan Akpabio Da Yahaya Bello

Next Post

An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

5 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

1 day ago
Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rawar Ganin Da BRICS Ke Takawa Wajen Samar Wa Kasashe Masu Tasowa ‘Yanci A Tsarin Gudanar Da Harkokin Kasa Da Kasa

3 days ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

1 week ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

1 week ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

1 week ago
Next Post
Sojoji Sun Kai Farmaki Masana’antar Kera Bindiga, Sun Yi Kame A Taraba

An Kashe 'Yan Ta'adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu - Hedikwatar Tsaro 

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

July 11, 2025
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.