• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kuma Fitar Da Sanarwar Xi’an A Yayin Taron Koli Tsakanin Kasar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Kuma Fitar Da Sanarwar Xi’an A Yayin Taron Koli Tsakanin Kasar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau Jumma’a da safe ne aka bude taron kolin kasar Sin da kasashen Tsakiyar Asiya karo na 1 a birnin Xi’an, babban birnin lardin Shaanxi da ke tsakiyar kasar Sin, inda shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya jagoranci taron, tare da gabatar da jawabi.

A cikin jawabinsa, Xi Jinping ya gabatar da ra’ayinsa kan yadda za a raya yankin tsakiyar Asiya, inda ya ce, tilas ne a kiyaye ikon mulki da tsaro, da ‘yanci da cikakkun yankunan kasashen yankin tsakiyar Asiya, kana a girmama hanyar da al’ummomin kasashen suka zaba da kansu wajen raya kasashensu, a goyi bayan kokarin yankin na tsakiyar Asiya na samun zaman lafiya, jituwa da kwanciyar hankali. Sa’an nan kuma, babu wanda ya isa ya tada rashin jituwa, da kuma adawa da juna a yankin tsakiyar Asiya, kana bai kamata a nemi samun ribar siyasa a yankin ba.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti

Dangane da gina al’ummomin Sin da tsakiyar Asiya mai makoma ta bai daya, Xi ya nuna cewa, wajibi ne bangarorin 2 su tsaya tsayin daga kan mara wa juna baya sosai a wasu muhimman al’amuran da suka shafi ikon mulkin kasa, ‘yancin kai, mutuncin al’umma, bunkasuwa cikin dogon lokaci da dai sauransu. Kana kuma wajibi ne su nemi samun bunkasuwa tare, su ci gaba da kasancewa a sahun gaba wajen aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”.

Har ila yau wajibi ne su tabbatar da tsaro dake shafar kowa, su nuna adawa da masu neman tsoma baki cikin harkokin cikin gidansu, da yunkurin yin juyin mulki, su kiyaye yaki da ‘yan a-ware, ‘yan ta’adda da masu tsattauran ra’ayi. Baya ga haka kuma, bangarorin 2 za su kiyaye dankon zumunci a tsakaninsu a nan gaba, da zurfafa yin koyi da juna ta fuskar wayewar kai.

Ban da haka kuma, shugaban na kasar Sin ya gabatar da shawarwari guda 8 kan hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya, wato kara kafa tsare-tsare, kyautata huldar tattalin arziki da ciniki, zurfafa hadewar juna, kara yin hadin gwiwa ta fuskar makamashi, kara azama kan yin kirkire-kirkire maras gurbata muhalli, inganta karfin bunkasuwa, kara yin tattaunawa ta fannin wayewar kai, da kiyaye zaman lafiya a yankin.

Labarai Masu Nasaba

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Kana shugabannin Sin da kasashe 5 na tsakiyar Asiya sun amince da kafa tsarin taron shugabannin kasashen, wanda za a shirya a kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya daya bayan daya a ko wadanne shekaru 2. Za a gudanar da taron kolin a kasar Kazakhstan a shekarar 2025. Haka kuma shugabannin sun amince da kafa ofishin sakatariya mai kula da tsarin kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya.

Bugu da kari, shugaban kasar Sin Xi Jinping, da shugabannin kasashen tsakiyar Asiya guda 5, sun sanya hannu kan “Sanarwar Xi’an”, tare da amincewa da jerin sakamakon da aka cimma a yayin taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya.

A Juma’a ne, aka kammala taron kwanaki biyu a birnin Xi’an na lardin Shaanxi dake yankin arewa maso yammacin kasar Sin. (Tasallah Yuan, Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Nada Oluwatoyin Madein A Matsayin Sabuwar Akanta-Janar

Next Post

Peng Liyuan Da Masu Dakin Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Biyu Sun Ziyarci Guyi Agency

Related

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

36 minutes ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

5 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

6 hours ago
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

7 hours ago
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 
Daga Birnin Sin

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

8 hours ago
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama
Daga Birnin Sin

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

8 hours ago
Next Post
Peng Liyuan Da Masu Dakin Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Biyu Sun Ziyarci Guyi Agency

Peng Liyuan Da Masu Dakin Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Biyu Sun Ziyarci Guyi Agency

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.