• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kuma Fitar Da Sanarwar Xi’an A Yayin Taron Koli Tsakanin Kasar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

by CMG Hausa
2 years ago
Asiya

Yau Jumma’a da safe ne aka bude taron kolin kasar Sin da kasashen Tsakiyar Asiya karo na 1 a birnin Xi’an, babban birnin lardin Shaanxi da ke tsakiyar kasar Sin, inda shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya jagoranci taron, tare da gabatar da jawabi.

A cikin jawabinsa, Xi Jinping ya gabatar da ra’ayinsa kan yadda za a raya yankin tsakiyar Asiya, inda ya ce, tilas ne a kiyaye ikon mulki da tsaro, da ‘yanci da cikakkun yankunan kasashen yankin tsakiyar Asiya, kana a girmama hanyar da al’ummomin kasashen suka zaba da kansu wajen raya kasashensu, a goyi bayan kokarin yankin na tsakiyar Asiya na samun zaman lafiya, jituwa da kwanciyar hankali. Sa’an nan kuma, babu wanda ya isa ya tada rashin jituwa, da kuma adawa da juna a yankin tsakiyar Asiya, kana bai kamata a nemi samun ribar siyasa a yankin ba.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti

Dangane da gina al’ummomin Sin da tsakiyar Asiya mai makoma ta bai daya, Xi ya nuna cewa, wajibi ne bangarorin 2 su tsaya tsayin daga kan mara wa juna baya sosai a wasu muhimman al’amuran da suka shafi ikon mulkin kasa, ‘yancin kai, mutuncin al’umma, bunkasuwa cikin dogon lokaci da dai sauransu. Kana kuma wajibi ne su nemi samun bunkasuwa tare, su ci gaba da kasancewa a sahun gaba wajen aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”.

Har ila yau wajibi ne su tabbatar da tsaro dake shafar kowa, su nuna adawa da masu neman tsoma baki cikin harkokin cikin gidansu, da yunkurin yin juyin mulki, su kiyaye yaki da ‘yan a-ware, ‘yan ta’adda da masu tsattauran ra’ayi. Baya ga haka kuma, bangarorin 2 za su kiyaye dankon zumunci a tsakaninsu a nan gaba, da zurfafa yin koyi da juna ta fuskar wayewar kai.

Ban da haka kuma, shugaban na kasar Sin ya gabatar da shawarwari guda 8 kan hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya, wato kara kafa tsare-tsare, kyautata huldar tattalin arziki da ciniki, zurfafa hadewar juna, kara yin hadin gwiwa ta fuskar makamashi, kara azama kan yin kirkire-kirkire maras gurbata muhalli, inganta karfin bunkasuwa, kara yin tattaunawa ta fannin wayewar kai, da kiyaye zaman lafiya a yankin.

LABARAI MASU NASABA

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Kana shugabannin Sin da kasashe 5 na tsakiyar Asiya sun amince da kafa tsarin taron shugabannin kasashen, wanda za a shirya a kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya daya bayan daya a ko wadanne shekaru 2. Za a gudanar da taron kolin a kasar Kazakhstan a shekarar 2025. Haka kuma shugabannin sun amince da kafa ofishin sakatariya mai kula da tsarin kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya.

Bugu da kari, shugaban kasar Sin Xi Jinping, da shugabannin kasashen tsakiyar Asiya guda 5, sun sanya hannu kan “Sanarwar Xi’an”, tare da amincewa da jerin sakamakon da aka cimma a yayin taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya.

A Juma’a ne, aka kammala taron kwanaki biyu a birnin Xi’an na lardin Shaanxi dake yankin arewa maso yammacin kasar Sin. (Tasallah Yuan, Ibrahim Yaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu
Daga Birnin Sin

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki
Daga Birnin Sin

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
Daga Birnin Sin

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Next Post
Peng Liyuan Da Masu Dakin Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Biyu Sun Ziyarci Guyi Agency

Peng Liyuan Da Masu Dakin Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Biyu Sun Ziyarci Guyi Agency

LABARAI MASU NASABA

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.