• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kuma Fitar Da Sanarwar Xi’an A Yayin Taron Koli Tsakanin Kasar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Kuma Fitar Da Sanarwar Xi’an A Yayin Taron Koli Tsakanin Kasar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau Jumma’a da safe ne aka bude taron kolin kasar Sin da kasashen Tsakiyar Asiya karo na 1 a birnin Xi’an, babban birnin lardin Shaanxi da ke tsakiyar kasar Sin, inda shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya jagoranci taron, tare da gabatar da jawabi.

A cikin jawabinsa, Xi Jinping ya gabatar da ra’ayinsa kan yadda za a raya yankin tsakiyar Asiya, inda ya ce, tilas ne a kiyaye ikon mulki da tsaro, da ‘yanci da cikakkun yankunan kasashen yankin tsakiyar Asiya, kana a girmama hanyar da al’ummomin kasashen suka zaba da kansu wajen raya kasashensu, a goyi bayan kokarin yankin na tsakiyar Asiya na samun zaman lafiya, jituwa da kwanciyar hankali. Sa’an nan kuma, babu wanda ya isa ya tada rashin jituwa, da kuma adawa da juna a yankin tsakiyar Asiya, kana bai kamata a nemi samun ribar siyasa a yankin ba.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti

Dangane da gina al’ummomin Sin da tsakiyar Asiya mai makoma ta bai daya, Xi ya nuna cewa, wajibi ne bangarorin 2 su tsaya tsayin daga kan mara wa juna baya sosai a wasu muhimman al’amuran da suka shafi ikon mulkin kasa, ‘yancin kai, mutuncin al’umma, bunkasuwa cikin dogon lokaci da dai sauransu. Kana kuma wajibi ne su nemi samun bunkasuwa tare, su ci gaba da kasancewa a sahun gaba wajen aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”.

Har ila yau wajibi ne su tabbatar da tsaro dake shafar kowa, su nuna adawa da masu neman tsoma baki cikin harkokin cikin gidansu, da yunkurin yin juyin mulki, su kiyaye yaki da ‘yan a-ware, ‘yan ta’adda da masu tsattauran ra’ayi. Baya ga haka kuma, bangarorin 2 za su kiyaye dankon zumunci a tsakaninsu a nan gaba, da zurfafa yin koyi da juna ta fuskar wayewar kai.

Ban da haka kuma, shugaban na kasar Sin ya gabatar da shawarwari guda 8 kan hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya, wato kara kafa tsare-tsare, kyautata huldar tattalin arziki da ciniki, zurfafa hadewar juna, kara yin hadin gwiwa ta fuskar makamashi, kara azama kan yin kirkire-kirkire maras gurbata muhalli, inganta karfin bunkasuwa, kara yin tattaunawa ta fannin wayewar kai, da kiyaye zaman lafiya a yankin.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

Kana shugabannin Sin da kasashe 5 na tsakiyar Asiya sun amince da kafa tsarin taron shugabannin kasashen, wanda za a shirya a kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya daya bayan daya a ko wadanne shekaru 2. Za a gudanar da taron kolin a kasar Kazakhstan a shekarar 2025. Haka kuma shugabannin sun amince da kafa ofishin sakatariya mai kula da tsarin kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya.

Bugu da kari, shugaban kasar Sin Xi Jinping, da shugabannin kasashen tsakiyar Asiya guda 5, sun sanya hannu kan “Sanarwar Xi’an”, tare da amincewa da jerin sakamakon da aka cimma a yayin taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya.

A Juma’a ne, aka kammala taron kwanaki biyu a birnin Xi’an na lardin Shaanxi dake yankin arewa maso yammacin kasar Sin. (Tasallah Yuan, Ibrahim Yaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Nada Oluwatoyin Madein A Matsayin Sabuwar Akanta-Janar

Next Post

Peng Liyuan Da Masu Dakin Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Biyu Sun Ziyarci Guyi Agency

Related

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

13 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

13 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

14 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

16 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

17 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

1 day ago
Next Post
Peng Liyuan Da Masu Dakin Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Biyu Sun Ziyarci Guyi Agency

Peng Liyuan Da Masu Dakin Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Biyu Sun Ziyarci Guyi Agency

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.