ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kuma Fitar Da Sanarwar Xi’an A Yayin Taron Koli Tsakanin Kasar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

by CMG Hausa
3 years ago
Asiya

Yau Jumma’a da safe ne aka bude taron kolin kasar Sin da kasashen Tsakiyar Asiya karo na 1 a birnin Xi’an, babban birnin lardin Shaanxi da ke tsakiyar kasar Sin, inda shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya jagoranci taron, tare da gabatar da jawabi.

A cikin jawabinsa, Xi Jinping ya gabatar da ra’ayinsa kan yadda za a raya yankin tsakiyar Asiya, inda ya ce, tilas ne a kiyaye ikon mulki da tsaro, da ‘yanci da cikakkun yankunan kasashen yankin tsakiyar Asiya, kana a girmama hanyar da al’ummomin kasashen suka zaba da kansu wajen raya kasashensu, a goyi bayan kokarin yankin na tsakiyar Asiya na samun zaman lafiya, jituwa da kwanciyar hankali. Sa’an nan kuma, babu wanda ya isa ya tada rashin jituwa, da kuma adawa da juna a yankin tsakiyar Asiya, kana bai kamata a nemi samun ribar siyasa a yankin ba.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti

Dangane da gina al’ummomin Sin da tsakiyar Asiya mai makoma ta bai daya, Xi ya nuna cewa, wajibi ne bangarorin 2 su tsaya tsayin daga kan mara wa juna baya sosai a wasu muhimman al’amuran da suka shafi ikon mulkin kasa, ‘yancin kai, mutuncin al’umma, bunkasuwa cikin dogon lokaci da dai sauransu. Kana kuma wajibi ne su nemi samun bunkasuwa tare, su ci gaba da kasancewa a sahun gaba wajen aiwatar da shawarar “ziri daya da hanya daya”.

ADVERTISEMENT

Har ila yau wajibi ne su tabbatar da tsaro dake shafar kowa, su nuna adawa da masu neman tsoma baki cikin harkokin cikin gidansu, da yunkurin yin juyin mulki, su kiyaye yaki da ‘yan a-ware, ‘yan ta’adda da masu tsattauran ra’ayi. Baya ga haka kuma, bangarorin 2 za su kiyaye dankon zumunci a tsakaninsu a nan gaba, da zurfafa yin koyi da juna ta fuskar wayewar kai.

Ban da haka kuma, shugaban na kasar Sin ya gabatar da shawarwari guda 8 kan hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya, wato kara kafa tsare-tsare, kyautata huldar tattalin arziki da ciniki, zurfafa hadewar juna, kara yin hadin gwiwa ta fuskar makamashi, kara azama kan yin kirkire-kirkire maras gurbata muhalli, inganta karfin bunkasuwa, kara yin tattaunawa ta fannin wayewar kai, da kiyaye zaman lafiya a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Kana shugabannin Sin da kasashe 5 na tsakiyar Asiya sun amince da kafa tsarin taron shugabannin kasashen, wanda za a shirya a kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya daya bayan daya a ko wadanne shekaru 2. Za a gudanar da taron kolin a kasar Kazakhstan a shekarar 2025. Haka kuma shugabannin sun amince da kafa ofishin sakatariya mai kula da tsarin kasar Sin da kasashen tsakiyar Asiya.

Bugu da kari, shugaban kasar Sin Xi Jinping, da shugabannin kasashen tsakiyar Asiya guda 5, sun sanya hannu kan “Sanarwar Xi’an”, tare da amincewa da jerin sakamakon da aka cimma a yayin taron kolin Sin da kasashen tsakiyar Asiya.

A Juma’a ne, aka kammala taron kwanaki biyu a birnin Xi’an na lardin Shaanxi dake yankin arewa maso yammacin kasar Sin. (Tasallah Yuan, Ibrahim Yaya)

Asiya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Next Post
Peng Liyuan Da Masu Dakin Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Biyu Sun Ziyarci Guyi Agency

Peng Liyuan Da Masu Dakin Shugabannin Kasashen Tsakiyar Asiya Biyu Sun Ziyarci Guyi Agency

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.