• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kunna Wutar Fara Gasar Olympics A Kasar Girka

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
An Kunna Wutar Fara Gasar Olympics A Kasar Girka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata aka kunna wutar gasar Olympics da Birnin Paris ke shirin karba nan da ‘yan makwanni kuma bikin na gargajiya ya gudana ne a garin Olympia mai tsohon tarihi da ke Girka, matakin da ke nuna kai wa gabar karshe na shirye-shiryen da aka shafe shekaru bakwai ana yi kan gasar da za a fara a ranar 26 ga Yuli.

Jarumar fina-finan kasar Girka Mary Mina, da aka zaba a matsayin jagorar bikin gargajiyar ce ta kunna wutar Olympics din, gasar da karo na uku kenan da Faransa za ta karbi bakuncinta a Birnin Paris bayan hakan da ta yi a shekarun 1900, da kuma 1924.

  • Sharhi: Kokarin Fahimtar Yanayin Tattalin Arzikin Sin Ta Bangarorin Ayyuka Guda 3
  • Mun Damu Da Matsalar Yara ‘Yan Shila A Adamawa – Fintiri

Yayin jawabin da ya gabatar shugaban kwamitin shirya gasar Olympics na duniya Thomas Bach, ya ce ko shakkah babu mutane sun kosa a fara wasannin motsa jikin domin debe musu kewa daga tashe-tashen hankulan da suke karuwa da suka kunshi, ta’addanci da kuma munanan labarai.

A makon da ya gabata shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce za a bukaci Rasha ta tsagaita bude wuta a Ukraine yayin gudanar gasar ta Olympics, kamar yadda aka saba mutunta wasannin a lokutan baya, sai dai Rasha ta ki amincewa da tsarin bisa zargin cewa Ukraine za ta iya amfani da damar wajen sake kintsawa yakin da suke gwabzawa.

Barazanar Tsaro:

Amma kuma a karon farko shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce za a iya sauya kogin Seine, da aka tsara gudanar da bikin bude gasar Olympics da Birnin Paris zai karbi bakunci, zuwa filin wasa na Stade de France saboda barazanar tsaro.

Kwamitin shirya gasar ta Olympics da Birnin Paris zai karbi bakunci dai ya shiya gudanar da gagarumin bikin bude gasar a kogin Seine, da a tarihi ba a taba yin irinsa a wajen filin da za a gudanar da wasannin gasar.

To sai dai gasar ta zo ne a dai-dai lokacin da ake fuskantar rikici tsakanin Rasha da Ukraine da kuma Isra’ila da Hamas a Gaza, lamarin da ya sanya hukumomin Faransa suka ce bikin bude gasar na cika da fuskantar barazanar hari.

A zantawar da aka yi da shugaba Macron a ranar Litinin din nan, ya ce suna da mabanbantan tsare-tsare da za su iya maye gurbin gudanar da bikin bude gasar a kogin Seine.

Labarai Masu Nasaba

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Akwai dai kimanin mutum dubu dari 3 da aka tsara su kasance a wajen bikin bude gasar, da kuma karin wasu dubu dari 2 da za su kalli bikin bude gasar daga gine-ginen da ke kusa da kogin Seine.

Kawo yanzu dukkanin kasashen da za su halarci gasar sun amince da kasancewa a bikin bude gasar da za a yi a Seine, cikinsu kuwa har da Amurka da Isra’ila da suka fi fuskantar barazana.

Sai dai shugaba Macron ya ce za su yi dukkanin abin da ya kamata, don ganin an samu tsaro da zaman lafiya a yayin gasar kamar yadda aka saba a kowacce shekara da kasar take karbar bakunci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Kara Haraji Kan Karafa Da Gorar Ruwa Dake Shiga Kasar Daga Kasar Sin

Next Post

Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Fara Da Kafar Dama A Farkon Bana

Related

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu
Wasanni

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

18 hours ago
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan
Wasanni

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

20 hours ago
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal
Wasanni

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

21 hours ago
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona
Wasanni

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

3 days ago
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG
Wasanni

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

4 days ago
Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5
Wasanni

Manchester United Ta Kammala Ɗaukar Cunha Daga Wolves Akan Miliyan 62.5

6 days ago
Next Post
Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Fara Da Kafar Dama A Farkon Bana

Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Fara Da Kafar Dama A Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.