ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kunna Wutar Fara Gasar Olympics A Kasar Girka

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Girka

A ranar Talata aka kunna wutar gasar Olympics da Birnin Paris ke shirin karba nan da ‘yan makwanni kuma bikin na gargajiya ya gudana ne a garin Olympia mai tsohon tarihi da ke Girka, matakin da ke nuna kai wa gabar karshe na shirye-shiryen da aka shafe shekaru bakwai ana yi kan gasar da za a fara a ranar 26 ga Yuli.

Jarumar fina-finan kasar Girka Mary Mina, da aka zaba a matsayin jagorar bikin gargajiyar ce ta kunna wutar Olympics din, gasar da karo na uku kenan da Faransa za ta karbi bakuncinta a Birnin Paris bayan hakan da ta yi a shekarun 1900, da kuma 1924.

  • Sharhi: Kokarin Fahimtar Yanayin Tattalin Arzikin Sin Ta Bangarorin Ayyuka Guda 3
  • Mun Damu Da Matsalar Yara ‘Yan Shila A Adamawa – Fintiri

Yayin jawabin da ya gabatar shugaban kwamitin shirya gasar Olympics na duniya Thomas Bach, ya ce ko shakkah babu mutane sun kosa a fara wasannin motsa jikin domin debe musu kewa daga tashe-tashen hankulan da suke karuwa da suka kunshi, ta’addanci da kuma munanan labarai.

A makon da ya gabata shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce za a bukaci Rasha ta tsagaita bude wuta a Ukraine yayin gudanar gasar ta Olympics, kamar yadda aka saba mutunta wasannin a lokutan baya, sai dai Rasha ta ki amincewa da tsarin bisa zargin cewa Ukraine za ta iya amfani da damar wajen sake kintsawa yakin da suke gwabzawa.

Barazanar Tsaro:

Amma kuma a karon farko shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce za a iya sauya kogin Seine, da aka tsara gudanar da bikin bude gasar Olympics da Birnin Paris zai karbi bakunci, zuwa filin wasa na Stade de France saboda barazanar tsaro.

Kwamitin shirya gasar ta Olympics da Birnin Paris zai karbi bakunci dai ya shiya gudanar da gagarumin bikin bude gasar a kogin Seine, da a tarihi ba a taba yin irinsa a wajen filin da za a gudanar da wasannin gasar.

ADVERTISEMENT

To sai dai gasar ta zo ne a dai-dai lokacin da ake fuskantar rikici tsakanin Rasha da Ukraine da kuma Isra’ila da Hamas a Gaza, lamarin da ya sanya hukumomin Faransa suka ce bikin bude gasar na cika da fuskantar barazanar hari.

A zantawar da aka yi da shugaba Macron a ranar Litinin din nan, ya ce suna da mabanbantan tsare-tsare da za su iya maye gurbin gudanar da bikin bude gasar a kogin Seine.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Akwai dai kimanin mutum dubu dari 3 da aka tsara su kasance a wajen bikin bude gasar, da kuma karin wasu dubu dari 2 da za su kalli bikin bude gasar daga gine-ginen da ke kusa da kogin Seine.

Kawo yanzu dukkanin kasashen da za su halarci gasar sun amince da kasancewa a bikin bude gasar da za a yi a Seine, cikinsu kuwa har da Amurka da Isra’ila da suka fi fuskantar barazana.

Sai dai shugaba Macron ya ce za su yi dukkanin abin da ya kamata, don ganin an samu tsaro da zaman lafiya a yayin gasar kamar yadda aka saba a kowacce shekara da kasar take karbar bakunci.

Girka
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Fara Da Kafar Dama A Farkon Bana

Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Fara Da Kafar Dama A Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.