• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Nada Sabbin Shugabannin Hisbah A Jihar Katsina

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Hisbah

Hukumar Hisbah a Jihar Katsina ta yi garanbawul a shugabancinta a matakin jiha tare da maye gurbin wasu sabbin shugabanni.

Bayanin hakan na kunshe ne cikin wata samarwa da sakataren hukumar, ya fitar aka raba wa manema labarai a Katsina.

  • An Gurfanar Da Wani Mutum A Kotu Kan Satar Dan Bunsuru 2
  • Abba Gida-Gida Ya Karbi Shaidar Lashe Zaben Gwamnan Kano

Sanarwar, ta ce tana sanar da al’umma game da wasu sauye-sauye da a ka samu a shugabancin Hisbah da suka shafi ofishin kwamandan jiha da magatakarda da kwamandan ladabtarwa da sauransu.

Hukumar ta ce ta maye gurbin tsohon kwamandan da Muhammad Rabi’u Garba, sai Abdullahi Yusuf a matsayin mataimakin kwamanda da kuma Muhammad Aminu Bello a matsayin magatakarda

Sauran sun hada da Muhammad Mahdi Rabi’u wanda ya maye gurbin kwamandan ladabtarwa sai kuma Abubakar Iliya a matsayin shugaban da’awa na Jihar Katsina.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Sanarwar ta ci gaba da bayanin cewa ta gode wa tsohon shugabanta na jiha Malam Hamisu Abubakar Imam a kan irin ci gaban da ya kawowa Hisbah a lokacinsa da kuma yi masa fatan nasara a rayuwarsa.

Haka kuma a jawabinsa sabon kwamandan Hisbah na Jihar Katsina, Muhammad Rabi’u Garba ya ba da tabbacin yin aiki tukuru ga al’ummar Jihar Katsina, da kuma kokarin kara bunkasa ayyukan Hisbah zuwa lunguna da sako-sako jihar.

Kazalika, ya taya zababben gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda murnar nasara da ya yi a zaben ranar Asabar 18 ga watan Maris, da yin addu’ar Allah SWT ya shige masa gaba a duk tsawon mulkinsa.

Sannan kuma yayi kira ga gwamnati mai zuwa da ta tabbatar da kafa hukumar Hisbah kamar yadda gwamnati mai barin gado ta Aminu Bello Masari ta yi.

Daga karshe shugaban ya taya dukkan Musulmai murnar shigowar watan Ramadan na shekara 1444 AH da fatan Allah SWT ya karbi dukkan ayyuka, da dacewa da alkairan da ke cikin wannan wata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman
Kananan Labarai

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

September 26, 2025
Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

May 23, 2025
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

April 18, 2025
Next Post
Fred M’membe:Shawarar Wayewar Kai Ta Duniya Za Ta Taimakawa Tabbatar Da Ci Gaban Duniya

Fred M’membe:Shawarar Wayewar Kai Ta Duniya Za Ta Taimakawa Tabbatar Da Ci Gaban Duniya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.