• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Rufe Rabin Masana’antun Kiwon Kifi A Jihar Filato

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
An Rufe Rabin Masana’antun Kiwon Kifi A Jihar Filato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar masu sana’ar kiwon Kifi ta kasa reshen jihar Filato ta bayyana cewa, kashi hamsin daga cikin dari na masana’tun kiwon Kifi a jihar sun garkame masana’antun, saboda kalubalen da suke fuskanta.

Shugaban kungiyar masana’antun Johnson Bagudu ne ya sanar da hakan, wanda kuma ya ce, fannin kiwon Kifi a jihar na matsayin daya daga cikin fannin da ke samar da ayyukan yi ga jama’a masu yawa.

  • Hadin Farfesun Kifi Na Zamani

Ya ci gaba da cewa, fiye da leburori 4,000, ke aiki a masana’antun, sai dai ya yi nuni da cewa, a yanzu, saboda dimbin kalubalen da suka dabaibaye su a jihar, kashi hamsin na masana’antunn an rufe su, wasu kuma ba sa yin sana’ar yadda suke bukata.

Bagudun ya bayyana hakan ne, a hirarsa da manema labarai a jihar, sannan kuma ya ce, wasu daga cikin manyan kalubalen da masana’antun ke fuskanta sun hada da, tsadar abincin na kiwon Kifayen da tsadar magunguna kula da lafiyarsu da rashin samun kasuwa.

A cewar Bagudu, a baya jihar Filato ta kasance a kan gaba wajen samar da Kifi a kasar nan, amma a yanzu irin wadannna kalubalen sun janyo komai yay a tsaya chak ga sana’ar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Bagudu, saboda haka ya ce, yanzu ya zama wajibi gwamnati ta kawo musu dauki, musamman ganin yadda fanin ke samar da dimbin ayyukan yi musamman ga matasan da ke a jihar.

“A baya jihar Filato ta kasance a kan gaba wajen samar da Kifi a kasar nan, amma a yanzu irin wadannna kalubalen sun jawo komai ya tsaya chik a sana’ar”.

Ya kara da cewa, wasu gwamnatocin jihohin da ke kasar nan, na tallfa wa masu sana’ar da ke a jihohinsu, inda ya bayar da misali da gwamnatin jihar Kano da ke tallafa wa masu sana’ar a jahar, musamman wajen sayen kwayayen da masana’antun jihar ke kyankyashe wa.

Shugaban ya sanar da cewa, kungiyar reshen jihar Filato, ba ta taba samun wani tallafi daga gun gwamnatin jihar ba, wanda ya kara da cewa, kungiyar ta mika sunayen ‘ya’yanta ga wasu hukumomi domin a tallafa musu, amma har yau babu wani tallafi da suka samu.

Ya ce, gwamnatin jihar na waiwaya masu sana’ar ce kawai idan aka samu aukuwar wata annoba, kamar ta murar tsintsaye saboda kauce wa shafar kiwon lafiyar al’ummar jihar.

“Kungiyar reshen jihar Filato, ba ta taba samun wani tallafi daga gun gwamnatin jihar ba, inda ya kara da cewa, kungiyar ta kuma mika sunayen ‘ya’yanta ga wasu hukumomi domin a tallafa masu, amma har yau babu wani tallafi da suka samu”.

Sai dai, Bagudu na da yakinin cewa, masu sana’ar na sa ran komai zai daidata, yadda za su fita daga cikin wannan kalubalen da suke fuskanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya

Next Post

Wasu Fasahohi Da Suka Taimaka Wa Rayuwar Al’umma A Bangarori Da Dama (I)

Related

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

4 days ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

4 days ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

2 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

2 weeks ago
Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 

2 weeks ago
Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
Noma Da Kiwo

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

2 weeks ago
Next Post
Wasu Fasahohi Da Suka Taimaka Wa Rayuwar Al’umma A Bangarori Da Dama (I)

Wasu Fasahohi Da Suka Taimaka Wa Rayuwar Al'umma A Bangarori Da Dama (I)

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.