• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Rufe Rabin Masana’antun Kiwon Kifi A Jihar Filato

by Abubakar Abba
3 years ago
Kifi

Kungiyar masu sana’ar kiwon Kifi ta kasa reshen jihar Filato ta bayyana cewa, kashi hamsin daga cikin dari na masana’tun kiwon Kifi a jihar sun garkame masana’antun, saboda kalubalen da suke fuskanta.

Shugaban kungiyar masana’antun Johnson Bagudu ne ya sanar da hakan, wanda kuma ya ce, fannin kiwon Kifi a jihar na matsayin daya daga cikin fannin da ke samar da ayyukan yi ga jama’a masu yawa.

  • Hadin Farfesun Kifi Na Zamani

Ya ci gaba da cewa, fiye da leburori 4,000, ke aiki a masana’antun, sai dai ya yi nuni da cewa, a yanzu, saboda dimbin kalubalen da suka dabaibaye su a jihar, kashi hamsin na masana’antunn an rufe su, wasu kuma ba sa yin sana’ar yadda suke bukata.

Bagudun ya bayyana hakan ne, a hirarsa da manema labarai a jihar, sannan kuma ya ce, wasu daga cikin manyan kalubalen da masana’antun ke fuskanta sun hada da, tsadar abincin na kiwon Kifayen da tsadar magunguna kula da lafiyarsu da rashin samun kasuwa.

A cewar Bagudu, a baya jihar Filato ta kasance a kan gaba wajen samar da Kifi a kasar nan, amma a yanzu irin wadannna kalubalen sun janyo komai yay a tsaya chak ga sana’ar.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Bagudu, saboda haka ya ce, yanzu ya zama wajibi gwamnati ta kawo musu dauki, musamman ganin yadda fanin ke samar da dimbin ayyukan yi musamman ga matasan da ke a jihar.

“A baya jihar Filato ta kasance a kan gaba wajen samar da Kifi a kasar nan, amma a yanzu irin wadannna kalubalen sun jawo komai ya tsaya chik a sana’ar”.

Ya kara da cewa, wasu gwamnatocin jihohin da ke kasar nan, na tallfa wa masu sana’ar da ke a jihohinsu, inda ya bayar da misali da gwamnatin jihar Kano da ke tallafa wa masu sana’ar a jahar, musamman wajen sayen kwayayen da masana’antun jihar ke kyankyashe wa.

Shugaban ya sanar da cewa, kungiyar reshen jihar Filato, ba ta taba samun wani tallafi daga gun gwamnatin jihar ba, wanda ya kara da cewa, kungiyar ta mika sunayen ‘ya’yanta ga wasu hukumomi domin a tallafa musu, amma har yau babu wani tallafi da suka samu.

Ya ce, gwamnatin jihar na waiwaya masu sana’ar ce kawai idan aka samu aukuwar wata annoba, kamar ta murar tsintsaye saboda kauce wa shafar kiwon lafiyar al’ummar jihar.

“Kungiyar reshen jihar Filato, ba ta taba samun wani tallafi daga gun gwamnatin jihar ba, inda ya kara da cewa, kungiyar ta kuma mika sunayen ‘ya’yanta ga wasu hukumomi domin a tallafa masu, amma har yau babu wani tallafi da suka samu”.

Sai dai, Bagudu na da yakinin cewa, masu sana’ar na sa ran komai zai daidata, yadda za su fita daga cikin wannan kalubalen da suke fuskanta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Wasu Fasahohi Da Suka Taimaka Wa Rayuwar Al’umma A Bangarori Da Dama (I)

Wasu Fasahohi Da Suka Taimaka Wa Rayuwar Al'umma A Bangarori Da Dama (I)

LABARAI MASU NASABA

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025
An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

An Samu Karuwar Sayayya Yayin Hutun Bikin Kafuwar Kasar Sin

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.