• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Rufe Rabin Masana’antun Kiwon Kifi A Jihar Filato

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
An Rufe Rabin Masana’antun Kiwon Kifi A Jihar Filato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar masu sana’ar kiwon Kifi ta kasa reshen jihar Filato ta bayyana cewa, kashi hamsin daga cikin dari na masana’tun kiwon Kifi a jihar sun garkame masana’antun, saboda kalubalen da suke fuskanta.

Shugaban kungiyar masana’antun Johnson Bagudu ne ya sanar da hakan, wanda kuma ya ce, fannin kiwon Kifi a jihar na matsayin daya daga cikin fannin da ke samar da ayyukan yi ga jama’a masu yawa.

  • Hadin Farfesun Kifi Na Zamani

Ya ci gaba da cewa, fiye da leburori 4,000, ke aiki a masana’antun, sai dai ya yi nuni da cewa, a yanzu, saboda dimbin kalubalen da suka dabaibaye su a jihar, kashi hamsin na masana’antunn an rufe su, wasu kuma ba sa yin sana’ar yadda suke bukata.

Bagudun ya bayyana hakan ne, a hirarsa da manema labarai a jihar, sannan kuma ya ce, wasu daga cikin manyan kalubalen da masana’antun ke fuskanta sun hada da, tsadar abincin na kiwon Kifayen da tsadar magunguna kula da lafiyarsu da rashin samun kasuwa.

A cewar Bagudu, a baya jihar Filato ta kasance a kan gaba wajen samar da Kifi a kasar nan, amma a yanzu irin wadannna kalubalen sun janyo komai yay a tsaya chak ga sana’ar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

Bagudu, saboda haka ya ce, yanzu ya zama wajibi gwamnati ta kawo musu dauki, musamman ganin yadda fanin ke samar da dimbin ayyukan yi musamman ga matasan da ke a jihar.

“A baya jihar Filato ta kasance a kan gaba wajen samar da Kifi a kasar nan, amma a yanzu irin wadannna kalubalen sun jawo komai ya tsaya chik a sana’ar”.

Ya kara da cewa, wasu gwamnatocin jihohin da ke kasar nan, na tallfa wa masu sana’ar da ke a jihohinsu, inda ya bayar da misali da gwamnatin jihar Kano da ke tallafa wa masu sana’ar a jahar, musamman wajen sayen kwayayen da masana’antun jihar ke kyankyashe wa.

Shugaban ya sanar da cewa, kungiyar reshen jihar Filato, ba ta taba samun wani tallafi daga gun gwamnatin jihar ba, wanda ya kara da cewa, kungiyar ta mika sunayen ‘ya’yanta ga wasu hukumomi domin a tallafa musu, amma har yau babu wani tallafi da suka samu.

Ya ce, gwamnatin jihar na waiwaya masu sana’ar ce kawai idan aka samu aukuwar wata annoba, kamar ta murar tsintsaye saboda kauce wa shafar kiwon lafiyar al’ummar jihar.

“Kungiyar reshen jihar Filato, ba ta taba samun wani tallafi daga gun gwamnatin jihar ba, inda ya kara da cewa, kungiyar ta kuma mika sunayen ‘ya’yanta ga wasu hukumomi domin a tallafa masu, amma har yau babu wani tallafi da suka samu”.

Sai dai, Bagudu na da yakinin cewa, masu sana’ar na sa ran komai zai daidata, yadda za su fita daga cikin wannan kalubalen da suke fuskanta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lambar Yabo Ta CON: Buni Ya Zama Zinare Bashi Da Maboya

Next Post

Wasu Fasahohi Da Suka Taimaka Wa Rayuwar Al’umma A Bangarori Da Dama (I)

Related

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

23 hours ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

1 day ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

1 week ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

1 week ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Next Post
Wasu Fasahohi Da Suka Taimaka Wa Rayuwar Al’umma A Bangarori Da Dama (I)

Wasu Fasahohi Da Suka Taimaka Wa Rayuwar Al'umma A Bangarori Da Dama (I)

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.