ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Rufe Rabin Masana’antun Kiwon Kifi A Jihar Filato

by Abubakar Abba
4 years ago
Kifi

Kungiyar masu sana’ar kiwon Kifi ta kasa reshen jihar Filato ta bayyana cewa, kashi hamsin daga cikin dari na masana’tun kiwon Kifi a jihar sun garkame masana’antun, saboda kalubalen da suke fuskanta.

Shugaban kungiyar masana’antun Johnson Bagudu ne ya sanar da hakan, wanda kuma ya ce, fannin kiwon Kifi a jihar na matsayin daya daga cikin fannin da ke samar da ayyukan yi ga jama’a masu yawa.

  • Hadin Farfesun Kifi Na Zamani

Ya ci gaba da cewa, fiye da leburori 4,000, ke aiki a masana’antun, sai dai ya yi nuni da cewa, a yanzu, saboda dimbin kalubalen da suka dabaibaye su a jihar, kashi hamsin na masana’antunn an rufe su, wasu kuma ba sa yin sana’ar yadda suke bukata.

ADVERTISEMENT

Bagudun ya bayyana hakan ne, a hirarsa da manema labarai a jihar, sannan kuma ya ce, wasu daga cikin manyan kalubalen da masana’antun ke fuskanta sun hada da, tsadar abincin na kiwon Kifayen da tsadar magunguna kula da lafiyarsu da rashin samun kasuwa.

A cewar Bagudu, a baya jihar Filato ta kasance a kan gaba wajen samar da Kifi a kasar nan, amma a yanzu irin wadannna kalubalen sun janyo komai yay a tsaya chak ga sana’ar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Bagudu, saboda haka ya ce, yanzu ya zama wajibi gwamnati ta kawo musu dauki, musamman ganin yadda fanin ke samar da dimbin ayyukan yi musamman ga matasan da ke a jihar.

“A baya jihar Filato ta kasance a kan gaba wajen samar da Kifi a kasar nan, amma a yanzu irin wadannna kalubalen sun jawo komai ya tsaya chik a sana’ar”.

Ya kara da cewa, wasu gwamnatocin jihohin da ke kasar nan, na tallfa wa masu sana’ar da ke a jihohinsu, inda ya bayar da misali da gwamnatin jihar Kano da ke tallafa wa masu sana’ar a jahar, musamman wajen sayen kwayayen da masana’antun jihar ke kyankyashe wa.

Shugaban ya sanar da cewa, kungiyar reshen jihar Filato, ba ta taba samun wani tallafi daga gun gwamnatin jihar ba, wanda ya kara da cewa, kungiyar ta mika sunayen ‘ya’yanta ga wasu hukumomi domin a tallafa musu, amma har yau babu wani tallafi da suka samu.

Ya ce, gwamnatin jihar na waiwaya masu sana’ar ce kawai idan aka samu aukuwar wata annoba, kamar ta murar tsintsaye saboda kauce wa shafar kiwon lafiyar al’ummar jihar.

“Kungiyar reshen jihar Filato, ba ta taba samun wani tallafi daga gun gwamnatin jihar ba, inda ya kara da cewa, kungiyar ta kuma mika sunayen ‘ya’yanta ga wasu hukumomi domin a tallafa masu, amma har yau babu wani tallafi da suka samu”.

Sai dai, Bagudu na da yakinin cewa, masu sana’ar na sa ran komai zai daidata, yadda za su fita daga cikin wannan kalubalen da suke fuskanta.

Kifi
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Wasu Fasahohi Da Suka Taimaka Wa Rayuwar Al’umma A Bangarori Da Dama (I)

Wasu Fasahohi Da Suka Taimaka Wa Rayuwar Al'umma A Bangarori Da Dama (I)

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.