ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Saki Ba’amurke Bayan Kuskuren Daure Shi Tsawon Shekara 28

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago

An saki wani dan kasar Amurka wanda aka yi kuskuren daurewa a gidan yari na tsawon shekara 28 a Missouri bayan zargin sa da laifin kisa, duk da ya sha musantawa.

A ranar Talata ne wani alkali Dabid Mason a kotun St Louis, ya yanke hukuncin da ya wanke mutumin mai suna Lamar Johnson, mai shekara 50.

  • Abin Da Ya Sa A Daminar Da Ta Gabata Masara Ta Yi Tsada -Shugaba
  • Tinubu Ya Isa Guinea-Bissau Domin Taron ECOWAS, Ya Ziyarci Sojojin Nijeriya

Alkalin ya ce ya yanke hukuncin ne bayan wasu shaidu biyu sun gabatar da gamsassun hujjoji da ya yadda da su da kuma suka nuna cewa mista Johnson ba shi da laifi.

ADVERTISEMENT

An yanke masa hukunci ne bayan da aka zarge shi da laifin kashe wani mai suna Marcus Boyd a shekarar 1994.

Magoya bayan mista Johnson sun yi ta sowa da murna da kuma tafi lokacin da kotu ta sanar da wanke shi.

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

 “Wannan abin farin ciki ne,” in ji mista Johnson, bayan barin cikin kotun.

 A bara ne wani babban alkali, Kim Gardner, ya shigar da kara inda yake bukatar a saki mista Johnson bayan kammala binciken wata kungiya da ya nuna mista Johnson ba shi da laifi.

Bayan hukuncin da aka yanke a ranar Talata, lauyoyin mista Johnson sun soki ofishin babban attoni janar na jihar da ya bukaci a ajiye shi a gidan yari.

 ‘Ofishin bai daina cewa Lamar ba shi da laifi ba, inda ma ba su damu ba ko da ya mutu a gidan yari,’’ in ji lauyoyin mista Jonson a cikin wata sanarwa da suka fitar.

Mai magana da yawun ofishin attoni janar din ya bayyana a cikin wani sako cewa ba zai dauki wani karin mataki ba kan lamarin.

 “Ofishinmu ya kare doka ne sannan kuma ya yi aiki domin tabbatar da an yi aiki da ainihin hukuncin da kwamitin lauyoyi ya yanke, bayan aiki da hujjojin da aka gabatar,’’ in ji sanarwar.

Wasu mutane biyu ne rufe da fuskokinsu suka harbe Marcus Boyd a gaban gidan mista Johnson a watan Oktoban 1994.

Mista Johnson ya sha nanata cewa ba ya gida a lokacin da aka far wa Marcus Boyd tare da kashe shi.

Alkali Mason ya yanke hukunci ne bayan da wani shaida ya soki bahasin da ya bayar, inda wani fursuna ya fadi gaskiyar cewa shi tare da wani mutum mai suna Phil Campbell suka harbe Boyd.

 Tun da farko a zaman jin karar, Campbell ya amsa cewa yana da laifi, amma ya roki a sassauta masa hukunci, inda aka yanke masa hukuncin daurin shekara bakwai a gidan yari.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna
Labarai

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 
Labarai

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
'yansanda
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Next Post
Rikicin Gabar Yammacin Kogin Jordan: Falasdinu Ta Kawo Karshen Hulda Da Isra’ila

Rikicin Gabar Yammacin Kogin Jordan: Falasdinu Ta Kawo Karshen Hulda Da Isra’ila

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.