ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Saki Ba’amurke Bayan Kuskuren Daure Shi Tsawon Shekara 28

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago

An saki wani dan kasar Amurka wanda aka yi kuskuren daurewa a gidan yari na tsawon shekara 28 a Missouri bayan zargin sa da laifin kisa, duk da ya sha musantawa.

A ranar Talata ne wani alkali Dabid Mason a kotun St Louis, ya yanke hukuncin da ya wanke mutumin mai suna Lamar Johnson, mai shekara 50.

  • Abin Da Ya Sa A Daminar Da Ta Gabata Masara Ta Yi Tsada -Shugaba
  • Tinubu Ya Isa Guinea-Bissau Domin Taron ECOWAS, Ya Ziyarci Sojojin Nijeriya

Alkalin ya ce ya yanke hukuncin ne bayan wasu shaidu biyu sun gabatar da gamsassun hujjoji da ya yadda da su da kuma suka nuna cewa mista Johnson ba shi da laifi.

ADVERTISEMENT

An yanke masa hukunci ne bayan da aka zarge shi da laifin kashe wani mai suna Marcus Boyd a shekarar 1994.

Magoya bayan mista Johnson sun yi ta sowa da murna da kuma tafi lokacin da kotu ta sanar da wanke shi.

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

 “Wannan abin farin ciki ne,” in ji mista Johnson, bayan barin cikin kotun.

 A bara ne wani babban alkali, Kim Gardner, ya shigar da kara inda yake bukatar a saki mista Johnson bayan kammala binciken wata kungiya da ya nuna mista Johnson ba shi da laifi.

Bayan hukuncin da aka yanke a ranar Talata, lauyoyin mista Johnson sun soki ofishin babban attoni janar na jihar da ya bukaci a ajiye shi a gidan yari.

 ‘Ofishin bai daina cewa Lamar ba shi da laifi ba, inda ma ba su damu ba ko da ya mutu a gidan yari,’’ in ji lauyoyin mista Jonson a cikin wata sanarwa da suka fitar.

Mai magana da yawun ofishin attoni janar din ya bayyana a cikin wani sako cewa ba zai dauki wani karin mataki ba kan lamarin.

 “Ofishinmu ya kare doka ne sannan kuma ya yi aiki domin tabbatar da an yi aiki da ainihin hukuncin da kwamitin lauyoyi ya yanke, bayan aiki da hujjojin da aka gabatar,’’ in ji sanarwar.

Wasu mutane biyu ne rufe da fuskokinsu suka harbe Marcus Boyd a gaban gidan mista Johnson a watan Oktoban 1994.

Mista Johnson ya sha nanata cewa ba ya gida a lokacin da aka far wa Marcus Boyd tare da kashe shi.

Alkali Mason ya yanke hukunci ne bayan da wani shaida ya soki bahasin da ya bayar, inda wani fursuna ya fadi gaskiyar cewa shi tare da wani mutum mai suna Phil Campbell suka harbe Boyd.

 Tun da farko a zaman jin karar, Campbell ya amsa cewa yana da laifi, amma ya roki a sassauta masa hukunci, inda aka yanke masa hukuncin daurin shekara bakwai a gidan yari.

Saki
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

MASU ALAKA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Next Post
Rikicin Gabar Yammacin Kogin Jordan: Falasdinu Ta Kawo Karshen Hulda Da Isra’ila

Rikicin Gabar Yammacin Kogin Jordan: Falasdinu Ta Kawo Karshen Hulda Da Isra’ila

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.