• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Rarrabuwa Kan Yunƙurin Barin Damagum A Matsayin Shugaban PDP Har Zuwa 2025

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
in Siyasa
0
An Samu Rarrabuwa Kan Yunƙurin Barin Damagum A Matsayin Shugaban PDP Har Zuwa 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gano wani yunkuri a cikin jam’iyyar adawa ta PDP na barin mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Iliya Damagum ya ci gba da rike mukaminsa har na tsawon wa’adin Dakta Iyorchia Ayu ya kare a 2025.

Duk da cewa tun da farko an tsayar da taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, taron gwamnonin jam’iyyar PDP da suka gudanar a Bauchi a karshen mako sun nuna cewa a dage zaben zuwa wani lokaci a cikin watan Fabrairun 2025, domin samun damar jam’iyyar ta warware matsalarta na ciki gida.

  • Yadda Gwamnonin PDP Suka Ceto Damagun Daga Kora
  • Online Payday Loans In Conrad, Montana Mt From Direct Lenders

Sai dai wasu majiyoyi sun shaida cewa matakin sauya shekar na kwamitin zartarwar nasara ce ga masu neman Damagum ya ci gaba da rike mukamin har zuwa karshen shekarar 2025.

Wata majiya ta ce tuni aka samu rabuwar kawuna, inda bangarori biyu suka kunno kai a cikin jam’iyyar PDP. Yayin da aka ce wani bangare wanda ya hada da wasu gwamnoni da masu ruwa da tsaki na kokarin ganin an tsawaita wa’adin zama a Damagum, dayan bangaren wanda kuma ya kunshi wasu gwamnoni da wasu masu fada ji na jam’iyyar suna aiki tukuru wajen ganin an zabi wani shugaban jam’iyya, wanda zai tabbatar da bin tsarin mulkin jam’iyyar kamar yadda aka saba a baya.

Damagum ya fito ne daga shiyyar arewa maso gabas, tun farko an zabe shi a matsayin mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa reshen arewa kafin ya hau kujerar mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, bayan tsige Dakta Iyorchia Ayu.

Labarai Masu Nasaba

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya nuna cewa dole ne wanda zai maye gurbin Ayu ya fito daga yanki da da shi, amma makirci ya mamaye jam’iyyar, wanda ya tabbatar da tsawaita jinkirin aiwatar da maye gurbin.

Wani shiri na samar da wanda zai maye gurbinsa daga arewa ta tsakiya ya ci karo da matsaloli bayan dage babban taron kwamitin zartarwa na jam’iyya da aka yi akai-akai. Taron na karshe da kwamitin zartarwa na jam’iyyar ta gudanar a ranar 18 ga watan Afrilu, an sanya ranar 15 ga watan Agusta domin gudanar da zaben shugaban jam’iyyar karo na 99, amma an dage taron da farko zuwa ranar 24 ga watan Oktoba, sannan zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, wanda a yanzu kungiyar gwamnonin na jam’iyyar ta kara dagawa.

Bincike ya nuna cewa yayin da masu neman maye gurbin Damagum ke neman wanda zai iya karbar ragamar mulki nan take, masu goyon bayan ci gaba da aikinsa a ofishin sun yi ta aiki a asirce kan yadda zai karasa sauran wa’adin Ayu, sannan kuma a sake zabensa a karo na biyu a 2025 don samun cikakken wa’adinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: PDP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Yi Garambawul Da Bullo Da Sabon Ci Gaban Kasuwancin Fasahohin Zamani

Next Post

Ƙasurguman ‘Yan Bindiga 7 Sun Mika Wuya Ga Sojoji

Related

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC
Siyasa

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

8 hours ago
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu
Siyasa

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

10 hours ago
Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami
Manyan Labarai

Mun Shirya Fuskantar APC Domin Ceto Talakawa – Abubakar Malami

20 hours ago
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar
Siyasa

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

1 day ago
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

2 days ago
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
Manyan Labarai

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

2 days ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Ƙasurguman 'Yan Bindiga 7 Sun Mika Wuya Ga Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.