ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Samu Rarrabuwa Kan Yunƙurin Barin Damagum A Matsayin Shugaban PDP Har Zuwa 2025

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

An gano wani yunkuri a cikin jam’iyyar adawa ta PDP na barin mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, Iliya Damagum ya ci gba da rike mukaminsa har na tsawon wa’adin Dakta Iyorchia Ayu ya kare a 2025.

Duk da cewa tun da farko an tsayar da taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, taron gwamnonin jam’iyyar PDP da suka gudanar a Bauchi a karshen mako sun nuna cewa a dage zaben zuwa wani lokaci a cikin watan Fabrairun 2025, domin samun damar jam’iyyar ta warware matsalarta na ciki gida.

  • Yadda Gwamnonin PDP Suka Ceto Damagun Daga Kora
  • Online Payday Loans In Conrad, Montana Mt From Direct Lenders

Sai dai wasu majiyoyi sun shaida cewa matakin sauya shekar na kwamitin zartarwar nasara ce ga masu neman Damagum ya ci gaba da rike mukamin har zuwa karshen shekarar 2025.

ADVERTISEMENT

Wata majiya ta ce tuni aka samu rabuwar kawuna, inda bangarori biyu suka kunno kai a cikin jam’iyyar PDP. Yayin da aka ce wani bangare wanda ya hada da wasu gwamnoni da masu ruwa da tsaki na kokarin ganin an tsawaita wa’adin zama a Damagum, dayan bangaren wanda kuma ya kunshi wasu gwamnoni da wasu masu fada ji na jam’iyyar suna aiki tukuru wajen ganin an zabi wani shugaban jam’iyya, wanda zai tabbatar da bin tsarin mulkin jam’iyyar kamar yadda aka saba a baya.

Damagum ya fito ne daga shiyyar arewa maso gabas, tun farko an zabe shi a matsayin mataimakin shugaban jam’iyyar na kasa reshen arewa kafin ya hau kujerar mukaddashin shugaban jam’iyyar na kasa, bayan tsige Dakta Iyorchia Ayu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

Kundin tsarin mulkin jam’iyyar ya nuna cewa dole ne wanda zai maye gurbin Ayu ya fito daga yanki da da shi, amma makirci ya mamaye jam’iyyar, wanda ya tabbatar da tsawaita jinkirin aiwatar da maye gurbin.

Wani shiri na samar da wanda zai maye gurbinsa daga arewa ta tsakiya ya ci karo da matsaloli bayan dage babban taron kwamitin zartarwa na jam’iyya da aka yi akai-akai. Taron na karshe da kwamitin zartarwa na jam’iyyar ta gudanar a ranar 18 ga watan Afrilu, an sanya ranar 15 ga watan Agusta domin gudanar da zaben shugaban jam’iyyar karo na 99, amma an dage taron da farko zuwa ranar 24 ga watan Oktoba, sannan zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba, wanda a yanzu kungiyar gwamnonin na jam’iyyar ta kara dagawa.

Bincike ya nuna cewa yayin da masu neman maye gurbin Damagum ke neman wanda zai iya karbar ragamar mulki nan take, masu goyon bayan ci gaba da aikinsa a ofishin sun yi ta aiki a asirce kan yadda zai karasa sauran wa’adin Ayu, sannan kuma a sake zabensa a karo na biyu a 2025 don samun cikakken wa’adinsa.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas

Ƙasurguman 'Yan Bindiga 7 Sun Mika Wuya Ga Sojoji

LABARAI MASU NASABA

PDP

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
PDP

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
PDP

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026
PDP

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.