ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnonin PDP Suka Ceto Damagun Daga Kora

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Rikicin gida a jam’iyyar PDP na daukar wani salo na daban, wanda a yanzu haka lamarin ya kazance, inda gwamnoni 9 daga cikin 13 na PDP da wasu jiga-jign jam’iyyar suka goyi bayan dakatar da shugaban riko na kasa na jam’iyyar PDP, Ambasada Umar Damagum.

Sobon rikicin ya kunno kai ne tun lokacin da wani bangare na jam’iyyar a wata sanarwa da Debo Ologunagba ya fitar, ya bayyana cewa ya dakatar da shugaban riko na kasa da kuma sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Samuel Anyanwu.

  • MOFA: Ministan Harkokin Wajen Birtaniya Zai Ziyarci Kasar Sin
  • Mambobin Kungiyar SCO Sun Bayyana Adawa Da Matakan Kariyar Cinikayya

Dakatarwar ya janyo cece-kuce a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar, inda a yanzu haka masu ruwa da tsaki na jam’iyyar na nemo hanyar dinke bakin zaren.

ADVERTISEMENT

Sai dai a sanarwar Ologunagba da ya fitar, ya ce an dakatar da Damagum da sakataren jam’iyyar na kasa, Sanata Anyanwu, saboda cin amanan jam’iyyar.

Ya ce an dakatar da su biyun ne saboda wasikar da suka aike wa kotun daukaka kara mai lamba: CA/PH/307/2024, kan matsayin jam’iyyar a shari’ar da ta shafi tsofaffin ‘yan majalisar dokokin Jihar Ribas su 27 da suka suka bar kujerunsu bayan sun fice daga PDP zuwa APC.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Saboda haka, kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ya yi amfani da sashi na 57, 58 da 59 na kundin tsarin mulkin PDP wajen dakatar da Amb. Illiya Damagum da Sanata Samuel Anyanwu a matsayinsu na shugaban riko na jam’iyyar na kasa da kuma sakataren jam’iyyar na kasa tare da mika su ga kwamitin ladabtarwa na jam’iyyar domin daukar mataki.

“A halin yanzu, an dakatar da jami’an biyu daga dukkan tarurrukan jam’iyya da ayyuka na jam’iyyar har sai an kwamitin ladabtarwa na kasa ya kammala bincike,” in ji shi.

Rahotanni sun tabbatar da cewa gwamnoni 9 na PDP sun amince da dakatar da Damagum daga mukaminsa na shugaban rikon jam’iyyar.

A cewar rahotanin, gwamnonin su ne Siminalayi Fubara (Jihar Ribas); Douye Diri (Jihar Bayelsa); Godwin Obaseki (Jihar Edo); Sheriff Francis Orohwedor Oborebwori (Jihar Delta); Agbu Kefas (Jhar Taraba); Dauda Lawal (Jihar Zamfara); Peter Mbah (Jihar Inugu); Ademola Adeleke (Jihar Osun) da Fasto Umo Eno (Jihar Akwa Ibom).

Rahotannin sun ce matakin ya biyo bayan wani taro da aka gudanar a ranar Asabar, inda gwamnonin suka amince da nadin Alhaji Ahmed Alaghi, ma’ajin jam’iyyar PDP na kasa a matsayin sabon shugaban riko na jam’iyyar.

An ruwaito cewa wani hadimi daga cikin gwamnonin yana jaddada kudirin gwamnonin na mutunta kundin tsarin mulkin jam’iyyar PDP da kuma warware rigingimun cikin gida ta saukakkiyar hanya.

Ya kara da cewa gwamnonin sun sake jaddada aniyarsu na gina jam’iyyar PDP da hadin kai tare da fifita muradun jam’iyyar sama da ra’ayin wani.

Sai dai mukaddashin jami’in yada labarai na jam’iyyar PDP, Ibrahim Abdullahi, ya karyata goyon bayan gwamnonin.

Ya ce wannan magana babu kamshin gaskiya a cikinta, babu wasu gwamnoni biyu da suka yi Magana ballantana a ce har gwamnoni 9 sun amince da wannan dakatarwar.

Tun da farko dai, jam’iyyar ta shirya gudanar da taronta na kasa a ranar 24 ga watan Oktoba, domin zaben sabon shugaban jam’iyyar na kasa wanda zai kammala wa’adin tsohon shugaban, Dakta Iyorchia Ayu.

Ana sa ran Damagum zai koma matsayinsa na baya na mataimakin shugaban jam’iyyar na arewa bayan kammala zaben.

Amma wata babbar kotun tarayya ta hana kwamitin gudanrwa da kwamitin zartarwa na PDP tsige shugaban riko na jam’iyyar. Sai dai kuma ba a saka kungiyar gwamnonin PDP cikin wannan hukuncin kotun ba.

Majiyoyi sun nuna cewa gwamnonin PDP na ta lalubo hanyoyin warware rikicin.

Wani jigon jam’iyyar da ya nemi a sakaye sunansa ya ce masu ruwa da tsaki a shiyyar arewa ta tsakiya ba za su iya jurewa abubuwan da ke faruwa a jam’iyyar na nuna son kai da kuma bujirewa tsarin mulkin jam’iyyar dangane da batun tsarin karba-karba a tsakanin shiyya-shiyya.

A cewarsa, babban abin da ‘ya’yan jam’iyyar PDP suka tsayu a kai shi ne, dole ne a karbo kujerar shugaban jam’iyyar daga wurin Damagum a mayar wa yankin arewa ta tsakiya.

Shi ma wani jigo a jam’iyyar, wanda kuma ya taba zama shugaban majalisar dokokin Jihar Filato a lokaci guda, Hon. Istifanus Mwansat, ya bai wa dattijai da dukkan shugabannin jam’iyyar da su tashi tsaye wajen gudanar da bin tsarin karba-karba a shugabancin jam’iyyar.

Sai dai kuma wasu ‘yan majalisar PDP sun bayyana matukar damuwarsu kan makircin tare da zargin APC da gwamnatin tarayya karkashin Shugaba Bola Tinubu kan kokarin mayar da Nijeriya tafarkin tsarin kasa mai jam’iyya daya.

PDP
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Yaya Kuri’un Yankin Arewa Maso Yamma Za Su Kasance A 2023?

Zaben Kananan Hukumomi: Gwamnoni Na Tozarta Dimokuradiyya – Jam’iyyun Adawa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.