ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shirya Bikin Yayata Shawarar Raya Kasa Da Kasa A Hedkwatar MDD

by CMG Hausa
3 years ago
MDD

A ranar Laraba 19 ga watan nan ne hukumar hadin gwiwa kan raya ci gaban kasa da kasa ta kasar Sin, da zaunanniyar tawagar wakilan kasar Sin dake MDD, da hukumomin MDD da abin ya shafa, suka shirya bikin yayata manufa cikin hadin gwiwa, mai taken “sabon salon ci gaban shawarar raya kasa da kasa, da sabon matakin ajandar tabbatar da ci gaba mai dorewa”. An gudanar da bikin ne a hedkwatar majalisar dake birnin New York na kasar Amurka.

Shugaban hukumar hadin gwiwa kan ci gaban kasa da kasa ta kasar Sin Luo Zhaohui, ya gabatar da muhimmin jawabi yayin bikin, inda ya bayyana cewa, muhimman shawarwarin da kasar Sin ta gabatar, kamar su gina kyakkyawar makomar bil Adam ta bai daya, da gina shawarar “ziri daya da hanya daya”, da raya kasa da kasa, sun gabatar da dabarun kasar Sin a fannin aikin sake farfadowar dukkanin duniya.

  • Bangaren Sin: Ya kamata Al’ummar Kasa Da Kasa Ta Goyi Bayan Kasashen Yankin Manyan Tabkuna Wajen Gina Makomar Bai Daya

Kaza lika makasudin kokarin ingiza zamanintarwa iri ta kasar Sin wanda kasar ke yi, shi ne samun ci gaba mai inganci, da bude kofa ga ketare bisa matsayin koli, kuma duk wadannan sun tattara fasahohi masu daraja, tare kuma da samar da dabaru na hikima da ake iya koya, karkashin muradun tabbatar da dauwamammen ci gaba.

ADVERTISEMENT

Luo ya jaddada cewa, idan ana fatan aiwatar da shawarar raya kasa da kasa, ya dace a cimma matsaya guda, a hada kai karkashin jagorancin MDD. A sa’i daya kuma, a gudanar da hadin gwiwa tsakanin kasashe masu ci gaba da kasashe masu tasowa.

Ya ce kasar Sin za ta ci gaba da bin tunanin gina kyakkyawar makomar bil Adam ta bai daya, domin kafa huldar abokantaka tsakanin kasa da kasa, ta yadda za a cimma burin raya kasa da kasa baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Sannan kakakin maaikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau cewa, kiran da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi, game da bukatar kiyaye tsaron duniya ya samu yabo da amincewa daga sassan kasa da kasa a cikin shekara guda, kuma ya zuwa yanzu, kasashe fiye da 80, da wasu kungiyoyin kasa da kasa sun nuna goyon baya ga hakan.

Wang Wenbin ya kara da cewa, Sin ta sa kaimi ga yin shawarwari game da kiyaye tsaro a tsakanin kasa da kasa, da sa kaimi ga kasashen nahiyar, wajen gudanar da taron farko na kiyaye zaman lafiya a tsakanin Sin da kasashen yankin kahon Afirka, inda suka cimma daidaito kan shimfida zaman lafiya, da samun bunkasuwa, da sarrafa harkokin kasa a yankin, tare da tabbatar da tsaron nahiyar Afirka baki daya.

Ban da wannan, kasar Sin ta kuma zaburar da bangarori daban daban, da su yi hadin gwiwa a fannonin yaki da cutar COVID-19, da yaki da taaddanci, da kiyaye halittu, da shaanin yanar gizo, da samar da hatsi, da batun sauyin yanayi da sauransu.

Wang Wenbin ya ce, Sin tana fatan yin kokari tare da bangarori daban daban, wajen rungumar tunanin kiyaye tsaro bisa tsarin bai daya, da raayoyin bangarori daban daban, da hada kai wajen tinkarar kalubalen tsaro, da sauran matsaloli da ba na tsaro ba, don sa kaimi ga samun zaman lafiya da bunkasuwar bil Adama tare. (Mai fassarawa: Jamila Zhou, Zainab Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa
Daga Birnin Sin

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
Next Post
Nijeriya Ta Sanya Hannu A Yarjejeniyar Amfani Da Fasahar Shuka Itatuwa Da Kasar Netherlands

Nijeriya Ta Sanya Hannu A Yarjejeniyar Amfani Da Fasahar Shuka Itatuwa Da Kasar Netherlands

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025
Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

Ana Ci Gaba Da Raya Kasar Sin Daga Matakin Kasa Mai Sauri Zuwa Kasa Mai Inganci

November 12, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki

November 12, 2025
Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

Kashi 74% Na Marasa Lafiya Sun Gamsu Da Ayyukan Kiwon Lafiya Na Nijeriya — Minista

November 12, 2025
Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.