ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Shirya Bikin Yayata Shawarar Raya Kasa Da Kasa A Hedkwatar MDD

by CMG Hausa
3 years ago
MDD

A ranar Laraba 19 ga watan nan ne hukumar hadin gwiwa kan raya ci gaban kasa da kasa ta kasar Sin, da zaunanniyar tawagar wakilan kasar Sin dake MDD, da hukumomin MDD da abin ya shafa, suka shirya bikin yayata manufa cikin hadin gwiwa, mai taken “sabon salon ci gaban shawarar raya kasa da kasa, da sabon matakin ajandar tabbatar da ci gaba mai dorewa”. An gudanar da bikin ne a hedkwatar majalisar dake birnin New York na kasar Amurka.

Shugaban hukumar hadin gwiwa kan ci gaban kasa da kasa ta kasar Sin Luo Zhaohui, ya gabatar da muhimmin jawabi yayin bikin, inda ya bayyana cewa, muhimman shawarwarin da kasar Sin ta gabatar, kamar su gina kyakkyawar makomar bil Adam ta bai daya, da gina shawarar “ziri daya da hanya daya”, da raya kasa da kasa, sun gabatar da dabarun kasar Sin a fannin aikin sake farfadowar dukkanin duniya.

  • Bangaren Sin: Ya kamata Al’ummar Kasa Da Kasa Ta Goyi Bayan Kasashen Yankin Manyan Tabkuna Wajen Gina Makomar Bai Daya

Kaza lika makasudin kokarin ingiza zamanintarwa iri ta kasar Sin wanda kasar ke yi, shi ne samun ci gaba mai inganci, da bude kofa ga ketare bisa matsayin koli, kuma duk wadannan sun tattara fasahohi masu daraja, tare kuma da samar da dabaru na hikima da ake iya koya, karkashin muradun tabbatar da dauwamammen ci gaba.

ADVERTISEMENT

Luo ya jaddada cewa, idan ana fatan aiwatar da shawarar raya kasa da kasa, ya dace a cimma matsaya guda, a hada kai karkashin jagorancin MDD. A sa’i daya kuma, a gudanar da hadin gwiwa tsakanin kasashe masu ci gaba da kasashe masu tasowa.

Ya ce kasar Sin za ta ci gaba da bin tunanin gina kyakkyawar makomar bil Adam ta bai daya, domin kafa huldar abokantaka tsakanin kasa da kasa, ta yadda za a cimma burin raya kasa da kasa baki daya.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Sannan kakakin maaikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau cewa, kiran da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi, game da bukatar kiyaye tsaron duniya ya samu yabo da amincewa daga sassan kasa da kasa a cikin shekara guda, kuma ya zuwa yanzu, kasashe fiye da 80, da wasu kungiyoyin kasa da kasa sun nuna goyon baya ga hakan.

Wang Wenbin ya kara da cewa, Sin ta sa kaimi ga yin shawarwari game da kiyaye tsaro a tsakanin kasa da kasa, da sa kaimi ga kasashen nahiyar, wajen gudanar da taron farko na kiyaye zaman lafiya a tsakanin Sin da kasashen yankin kahon Afirka, inda suka cimma daidaito kan shimfida zaman lafiya, da samun bunkasuwa, da sarrafa harkokin kasa a yankin, tare da tabbatar da tsaron nahiyar Afirka baki daya.

Ban da wannan, kasar Sin ta kuma zaburar da bangarori daban daban, da su yi hadin gwiwa a fannonin yaki da cutar COVID-19, da yaki da taaddanci, da kiyaye halittu, da shaanin yanar gizo, da samar da hatsi, da batun sauyin yanayi da sauransu.

Wang Wenbin ya ce, Sin tana fatan yin kokari tare da bangarori daban daban, wajen rungumar tunanin kiyaye tsaro bisa tsarin bai daya, da raayoyin bangarori daban daban, da hada kai wajen tinkarar kalubalen tsaro, da sauran matsaloli da ba na tsaro ba, don sa kaimi ga samun zaman lafiya da bunkasuwar bil Adama tare. (Mai fassarawa: Jamila Zhou, Zainab Zhang)

MDD
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Nijeriya Ta Sanya Hannu A Yarjejeniyar Amfani Da Fasahar Shuka Itatuwa Da Kasar Netherlands

Nijeriya Ta Sanya Hannu A Yarjejeniyar Amfani Da Fasahar Shuka Itatuwa Da Kasar Netherlands

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.