ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Tsinci Gawar Mutum 9 Da Hatsarin Kwale-kwale Ya Rutsa Da Su A Jihar Neje – NSEMA

by Muhammad
2 years ago
Kwale-kwale

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Neja, NSEMA, ta ce an gano gawar mutum 9 da wani hatsarin kwale-kwale da ya rutsa da su a karamar hukumar Shiroro ta jihar Neja.

Shugaban Hukumar bayar da agaji ta (NSEMA), Alhaji Salihu Garba, ne ya bayyana hakan a wata tattaunawa da ya yi da manema Labarai a Minna ranar Lahadi.

  • Hatsarin Kwale-kwale Ya Yi Sanadin Rasuwar Mutum 2 A Jihar Neja
  • Kifewar Kwale-kwale Na Ci Gaba Da Salwantar Da Rayukan ‘Yan Nijeriya

Rahotanni sun tabbatar da mutuwar mutum goma a wani hatsarin kwale-kwale da ya afku a ranar Alhamis, 16 ga watan Nuwamba.

ADVERTISEMENT

Kazalika, rahotannin sun bayyana cewa wadanda abin ya rutsa da su ‘yan kasuwa ne, suna jigilar kaya ne daga unguwar Zongoru da ke yankin Bassa zuwa Gijiwa kusa da kasuwar Juma’a da ke Kuta, hedikwatar karamar hukumar Shiroro.

Akalla mutum 34 ne suke cikin jirgin wanda 10 daga cikinsu suka rasa rayukansu, yayin da aka kubutar da mutum 22.

LABARAI MASU NASABA

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

Garba ya bayyana sunayen wadanda suka rasu, sun hada da Farida Muntari da Sharhabila Sagir da Bubakar Sadiq da Na’ima Ibrahim da Amina da Safaratu Ibrahim da Sadiq Ibrahim da kuma Rafiya Yakubu.

Ya ce har yanzu hukumar ba ta tantance biyu daga cikin mutanen da suka mutu ba, ya kara da cewa dukkan wadanda suka mutu ‘yan garin Zangoro ne.

Garba ya ce, akwai maza da mata manya 24 da kuma yara maza da mata 10 a cikin jirgin a lokacin da ya kife.

Garba ya kuma ce ana ci gaba da bincike don gano sauran gawarwakin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ECOWAS
Labarai

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe
Labarai

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Kwankwaso
Labarai

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Next Post
Gwamnan Jihar Filato Zai Garzaya Kotun Ƙoli Don Ƙalubalantar Hukuncin Soke Zaɓensa

Gwamnan Jihar Filato Zai Garzaya Kotun Ƙoli Don Ƙalubalantar Hukuncin Soke Zaɓensa

LABARAI MASU NASABA

ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.