• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Bikin Cikar Sarkin Lafiyan Bare-bari Shekaru 5 A Kan Karagar Mulki A Nasarawa

by Zubairu M Lawal
1 year ago
in Al'adu, Al'ajabi, Labarai, Masarautu
0
An Yi Bikin Cikar Sarkin Lafiyan Bare-bari Shekaru 5 A Kan Karagar Mulki A Nasarawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Asabar 4/5/2024 Sarkin Lafian Bare-bari tsohon mai Shari’a, Sidi Bage Muhammad, ya gudanar da gagarumin taron bikin murnar cika shekaru biyar kan karagar mulkin masarautar Lafiyan Bare-bari ta jihar Nasarawa.

Taron da ya samu halartar manyan sarakuna daga kowane sassa a fadin Nijariya.

  • Gwamatin Tarayya Ta Fito Da Tsarin Cin Gajiyar Ma’adanan da Ke Jihar Nasarawa
  • Karancin Wuta: Majalisar Dokokin Nasarawa Ta Bai Wa AEDC Makonni 2 Don Gyara Wutar Lantarki

Da yake jawabi a wurin taron, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya ce, wannan taron ya nuna wa duniya cewa sarakuna suna kokari wajan tabbatar da Nijariya a matsayinta na dunkulalliyar kasa.

Sultan ya ce, a wannan taron sarakuna daga sassa daban-daban na Nijariya sun halarta domin nuna farin ciki da tabbatar da zaman lafiyar Nijariya.

Surkin Musulmi ya ce, sau da yawa mutane suna zagin shugabanni su ce basa yin aikin komai, alhalin lokacin da ake aikin mutane can suna barci.

Labarai Masu Nasaba

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Sultan yayi kira ga ‘yan Nijariya da su dage da yi wa shugabanni addu’ar kwarai domin samun ci gaban Nijariya.

Shi ma a nasa jawabin, Shehun Borno, Ibin Umar Abubakar El-Kanami, ya yi fatan Allah ya kara hada kan yan Nijariya ya budawa kowa a hanyar sana’arsa.

Ya bukaci al’umma da su zama masu taimakawa jami’an tsaro da bayanan sirri wajen fallasa ‘yan ta’adda a duk inda suke.

Gwamnan jihar Nasarawa. Abdullahi Sule, ya godewa dukkanin sarakuna da suka baro jihohinsu suka zo Jihar Nasarawa don halartar wannan taro.

Bayan kammala taron manyan baki sun shiga cikin fada domin bude gidan tarihi na jerin sarakuna sha bakwai da suka mulki masarautar Lafiyan Bare-bari wanda Sarki Sidi Bage Muhammad ya gina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Lafiyar Bare-bariNasarawaNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (6)

Next Post

Kamfanoni 530 Suka Nuna Bukatar Neman Aikin Gyaran Jiragen Kasan Nijeriya Na Naira Biliyan 11

Related

Zamfara
Manyan Labarai

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 

17 minutes ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

2 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

3 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

4 hours ago
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
Manyan Labarai

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

6 hours ago
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara
Labarai

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

7 hours ago
Next Post
Kamfanoni 530 Suka Nuna Bukatar Neman Aikin Gyaran Jiragen Kasan Nijeriya Na Naira Biliyan 11

Kamfanoni 530 Suka Nuna Bukatar Neman Aikin Gyaran Jiragen Kasan Nijeriya Na Naira Biliyan 11

LABARAI MASU NASABA

Zamfara

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

September 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

September 15, 2025
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

September 15, 2025
Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

September 15, 2025
KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano

September 15, 2025
Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara

September 15, 2025
Barcelona Ta FarfaÉ—o Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

Barcelona Ta FarfaÉ—o Zuwa Matsayi Na Biyu Bayan Lallasa Valencia A Johan Cruyff

September 15, 2025
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.