• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Falastinu A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Falastinu

A Juma’ar nan ne dubban jama’a suka fito kan titi inda suka zagaye gari da nufin nuna goyon bayansu ga al’umman Palastinu wanda Yahudawa ke zalumta kamar yanda masu gangamin suka bayyana.

 

Malam Ahmad Yusuf Yashi, wakilin ‘yan uwa musulmai almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky na jihar Bauchi ne ya jagoranci masu zagayen garin, ya bayyana cewar sun fito ne domin amsa kiran Ayyatullahi Imam Khumaini na kiran illahirin jama’a da suke amfani da ranar Juma’ar karshen ramadana wajen tunawa da raunanan Palasdinawa da kuma sauran wadanda ake zalumta a fadin duniya.

  • Likitoci Sun Ja Daga A Kan Dokar Yin Aiki Na Shekara Biyar

“Shi wannan massalacin na Quds shi ne masallaci na uku a daraja amma an wayi gari yana karqashin ikon Yahudawan Sahayoniya kuma wajibi ne mu kwato wannan massalacin domin na musulmai ne,” a cewarsa

 

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Ya kuma qara da cewa a irin wannan ranar su na kuma tuna da kuma yin dubiya kan halin da sauran jama’an duniya ke ciki musamman wadanda ake zalumta.

 

A cewar Ahmad Yashi sun fito ne domin su goyi bayan al’ummar Falastinu tare da tir da zalumcin da Yahudawa ke yi wa al’ummar Falastinuwa, ya nuna cewa shirin Yahudawa ba ga zallar Falastinuwa ya tsaya ba so suke su mamaye yankin Gabas ta tsakiya baki daya.

 

Ya ce: “Wannan fitowa da muke yi ba ma ga zallar Falastinuwa ba ne, a gaskiyar magana don dukkanin musulman duniya da raunanan da suke rayuwa a doron kasa. Domin da Isra’ila za ta yi nasara kawar da wadanda suke Palastinu to za ta mamaye dukkanin Gabas ta Tsakiya ne, wadannan kasashen irinsu Lebonon, Siriya, Jordan, Yusra da makamantansu. Domin ta taba gwada wannan yunkurin nata a 1967 na mamaye sassan wadannan wuraren.

 

“Su na nan suna da wannan tunanin da wannan burin. A takaice ma har sun bai wa shirinsu suna da cewa za su samar da Isra’ila babba wanda sun ce za su hada har da Madina daman sun ce Madina kasarsu ce, Annabi da ya zo ne ya koresu a nan.

 

“Don haka ya kamata musulmai su shiga cikin hayyacinsu ba magana ce ta ‘yan Shi’a ko ‘yan kaza ba. A’a lamari ne da ya shafi musulman duniya baki daya da duk kuma wanda yake da rauni a doron kasa. Kiranmu a nan shi ne al’umma ta zo da Sunnanta da Shi’anta a fito a yi Allah wadai da abun da Yahudawa ke yi a wannan yankin da kuma nuna goyon baya ga al’ummar Falastinu. Kuma insha Allahu nasara na nan tafe ga al’ummar Falastinu,” ya tabbatar.

 

Wakilinmu da ya kasance da muzaharar ya shaida mana cewar masu muzaharar sun yi ta waken bayyana halin da al’ummar Falasdinawa ke ciki, da kuma nuna goyon bayansu a garesu. An yi zagayen lafiya aka kuma tashi a cikin garin na Bauchi

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani
Daga Birnin Sin

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Next Post
Yadda Za Ki Tsara Kwalliyarki Ranar Sallah

Yadda Za Ki Tsara Kwalliyarki Ranar Sallah

LABARAI MASU NASABA

Falastinu

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.