• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Garkuwa Da Dalibai 1,680 Da Kashe 180 Cikin Shekara 10 A Nijeriya – UNICEF

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Labarai
0
An Yi Garkuwa Da Dalibai 1,680 Da Kashe 180 Cikin Shekara 10 A Nijeriya – UNICEF
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya bayyana cewa an yi garkuwa da yara 1,680 yayin da kuma 180 daga cikinsu an kashe su ne tun lokacin da aka fara garkuwa da ‘yan makarantar mata a Nijeriya a shekarar 2014.

Wani sabon rahoton da asusun ya fitar na cewa kashi 37 ne kawai na makarantu daga jihohi 10 aka bayyana masu alamu masu tayar da hankali don su gane kamar kawo wa makaranta hari.

  • Sauyin Yanayi: Dabarun Da  Za Su Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi
  • An Lalata Haramtattun Rijyoyin Mai 7 Da Jiragen Ruwa 4 A Ribas

Hakan yana kasancewa ne yayin da Nijeriya cika shekara 10 tun lokacin da aka fara garkuwa da ‘yan makaranta masu yawa, inda ‘yan mata 91 a Arewa maso gabas har yanzu ana ci gaba da garkuwa da su,yayin da Nijeriya ke kara shiga wani alhini na ‘yan makarantar Kaduna wanda aka yi a watan Maris na wannan shekarar.

UNICEF ya yi kira da a daukai matakan da suka dace wajen kare kananan yara wadanda sune abin ya fi shafa.

“Dauka da garkuwa da ‘yan matan a makarantar Chibok wani jirwaye mai kamar wanka ne, mai nuna irin hadarin da yara ke shiga a kokarin da suke wajen neman Ilimi,”Ms Cristian Munduate wakiliyar UNICEF a Nijeriya ta ce lokacin da ake gabatar da rahoton a ofishin Majalisar Dinkin Duniya.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ta ce a yau da ake tunawa da abin bakincikin na garkuwar da aka yi a sassa daban-daban na Nijeriya, “Hakan wata manuniya ce a kokarin da muke yi  domin kare lafiyar ‘ya’yanmu”.Wadannan alkalumma masu ta da hankali ba wai za mu tsaya kan alamu ba har ma abubuwan da suke sa ana samun su tashin hankalin da kan shiga.

“Ilimi wata dama ce da ake bi domin fita daga fatara, sai dai duk da hakan yawan kananan yara a Nijeriya har yanzu sun kasa cimma burinsu.

“Abin ya taso ne bayan wasu bayanai da aka samu na rahotanni masu ta da hankali na tashe- tashen hankula a makaranta da suka shafi garkuwa da dalibai lamarin da yake karuwa.

“Shekaru 10 da suka wuce an samu yin garkuwa da yara 1,680 lokacin da suke makaranta da wasu wurare, an kuma kashe 180 saboda harin da ake ka iwa makarantu, inda aka kiyasta an yi garkuwa da malamai 60 aka kashe 14, fiye da hari 70 da aka kai wa makarantu kamar yadda rahoton da aka tabbatar da sahihanci shi na Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana.”

Babbar jami’ar Ilimi, Saadhna Panday-Soobrayan ta bayyana haka ne a ofishin hukumar UNICEF lokacin da take bayar da rahoto a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tarkunan Da Aka Dana Wa Ganduje A Kano

Next Post

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)

Related

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta
Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

2 hours ago
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina
Labarai

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

3 hours ago
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

4 hours ago
Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

14 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

15 hours ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

18 hours ago
Next Post
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

August 25, 2025
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

August 25, 2025

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

August 24, 2025
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

August 24, 2025
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

August 24, 2025
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

August 24, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

August 24, 2025
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

August 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.