ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
Lalata

Al’ummomi a sassan Nijeriya na fama da mummunan tasirin ambaliyar ruwa da ta lalata gadaje da hanyoyi, ta hana zirga-zirgar mutane da kaya, tare da haifar da ƙarin wahalhalu ga jama’a. Binciken Jaridar Daily Trust ya gano cewa yawancin waɗannan gadoji da hanyoyi sun daɗewa ba tare da kulawa ko gyara ba kafin su rushe.

Gadar Kufai Ta Filato Ta Rushe

A Jihar Filato, rushewar Gadar Kufai dake kusa da ƙauyen Yelwa a ƙaramar hukumar Shendam ta jefa mazauna yankin cikin halin ƙunci. Gadar, wadda aka gina shekaru fiye da talatin da suka gabata, tana da muhimmanci ga matafiya da masu safarar kaya daga Plateau zuwa jihohin Nasarawa da Taraba, da ma direbobin manyan motoci dake kai kayan abinci zuwa Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma.

ADVERTISEMENT
  • Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

Gadar ta fara rushewa a shekarar 2022, sannan aka yi mata ɗan gyaran wucin-gadi a bana. Amma ruwan sama mai ƙarfi ya sake wanke ta a watan Agusta.

Mazauna yankin sun koka cewa gwamnati ta manta da su.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

“Rushewar wannan gada na haifar mana da matsala sosai. Gwamnati ta taimaka ta gyara,” in ji Wayu Bamga, mazaunin yankin.

Nanlong Nyas ya ƙara da cewa, “Gyaran da aka yi bai daɗe ba kafin ruwa ya sake lalata gadar.”

Wasu direbobi kamar Umar Sa’adu da Abubakar Haruna sun ce duk lokacin da suka isa wurin gadar, sai sun biya ma’aikata su tura motarsu kafin su iya tsallaka rafi kana su ci gaba da tafiya.

Rushewar Gadar Namne Ta Taraba Ta Tsayar Da Zirga-Zirga

A Jihar Taraba kuwa, Gadar Namne dake kan hanyar Jalingo–Wukari  ta rushe a watan Agustan 2024 bayan ruwan sama mai yawa, kuma har yanzu shekara guda bayan haka, babu wani gyara da gwamnatin tarayya ko ta jiha ta fara.

Gadar tana da muhimmanci sosai saboda tana haɗa Arewa maso Gabas da Kudu maso Gabas, Kudu maso Yamma da kuma babban birnin Tarayya (Abuja). Duk da alƙawarin da Gwamna Agbu Kefas, da gwamnatin tarayya da hukumar ci gaban Arewa Maso Gabas (North-East Development Commission (NEDC) suka yi, babu wani aikin gyara da aka fara har yanzu.

A yanzu, matafiya suna amfani da kwale-kwale wajen tsallaka kogin, yayin da ƙananan motoci da babura ne kawai ke iya bin hanyar. Ana kuma cajin matafiya kuɗi don tsallaka kogin.

“Farashin sufuri da kayan masarufi sun tashi saboda doguwar hanya da direbobi ke bi,” in ji wani mazaunin yankin. “Tsallaka rafi da kwale-kwalen  kuma na da hatsari, musamman ga waɗanda ba su saba ba.”

Tasirin A ƙasa baki ɗaya

A wasu jihohi kamar Kebbi, da Kogi da Neja, irin wannan ambaliya ta lalata gadoji da hanyoyi, ta katse alaƙa tsakanin ƙauyuka da birane, ta kuma jawo cikas ga harkokin kasuwanci da tattalin arziƙi.

Masana harkokin gine-gine da muhalli sun yi gargaɗi cewa, sai an samar da tsarin ƙasa baki ɗaya na magance ambaliya da kuma yin gadaje da hanyoyi masu jure ruwa, idan ba haka ba, za a ci gaba da fuskantar irin wannan ɓarnar kowace shekara.

Lalata
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.