• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Matashi Daurin Rai Da Rai Kan Yi Wa Kurma Fyade A Kebbi

by Umar Faruk
1 year ago
in Labarai
0
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar kotun Jihar Kebbi, mai lamba shida a karkashin jagorancin Mai shari’a Maryam Abubakar- Kaoje, ta yanke wa wani matashi mai suna Jamilu Abdullahi da ke kauyen Dan-Warai a Karamar Hukumar Aliero hukuncin daurin rai da rai kan yi wa wata yarinya ‘yar shekara takwas da haihuwa a duniya fyade wanda yarinyar kurma ce.

Lauyan masu shigar da kara, Barista Zainab Jabbo, a nata jawabin, ta ce wanda ake tuhumar mai shekaru 13 yana fuskantar tuhuma guda daya ne kan aikata laifin fyade.

  • ‘Yan Fashi Sun Kashe Wani Dan Kasuwa A Bayelsa
  • Wasu A NNPC Ba Su So Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Kare – Sarki Sanusi

Ya aikata laifin ne a ranar 19 ga Watan Junairun 2023 a kauyen Dan-Warai da ke karamar hukumar Aliero a jihar.

“Wadda ta roki kotun da ta yanke wa wanda ake tuhumar hukuncin da ya kama ta bisa dokar da ake tuhumarsa a kai, wanda ya yaudare ta zuwa wani gini da ba a kammala ba, inda ya yi mata fyade ta hanyar sanya zakarinsa cikin farginta ba tare da yardata ba,” in ji ta.

Barista Zainab Jabbo ta roki kotu da ta hukunta wanda ake tuhuma, saboda doka ta sanya hukuncin kan tilas.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Laifin fyaden yana da hukunci a karkashin sashe na 210 na dokar Penal Code na Jihar Kebbi na 2021.

Mai gabatar da kara ta kira da kuma gabatar da shaidu biyar, sannan ta gabatar da takardu kara shaida na tabbatar da cewa wanda ake tuhumar ya aikata laifin.

A nasa bangaren, lauyan da ke ba da kariya ga wanda ake tuhumar a gaban kotun, Barista Bashar Zakari, ya kira wanda ake tuhumar da ya bayar da shaida domin kare kansa a gaban kotun.

Haka kuma lauyan ya roki kotun da ta yi wa wanda ake kara adalci a lokacin da za ta yanke hukuncinta.

A cikin hukuncin kotun, Mai Shari’a Maryam Abubakar-Kaoje, ta bayyana cewa kotun ta samu wanda ake kara da laifin aikata laifin fyade.

Kotun ta ce masu gabatar da kara sun tabbatar da duk abubuwan da ke nuna cewa ya aikita laifin da ake tuhumarsa.

Mai shari’a Maryam Kaoje, yayin da ta bayyana laifin a matsayin “mummuna”, ta kuma bayyana cewa wanda ake tuhumar ya yi amfani da rauninta wadda aka yi wa fyaden kuma ya ci amanar yarinyar ta hanyar aikata laifin fyaden.

“Bayan an same ka da laifin da ake tuhumarka da shi a gaban wannan kotun, kotu ta yanke maka hukuncin daurin rai da rai saboda samunka da laifin lalata wata yarinya ‘yar shekara takwas da ke zaune a garin Dan-Warai a Karamar Hukumar Aliero a Jihar ta Kebbi wanda ka aikata tun a ranar 19 ga Watan Janairu shekarar 2023.

“Wannan hukuncin zai hana wasu da za su yi tunanin aikata irin wannan laifi,” in ji ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FyadeKebbiKotuKurma
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Fashi Sun Kashe Wani Dan Kasuwa A Bayelsa

Next Post

An Kama Mutane 2 Da Laifin Kashe Wani Mutum Kan ‘Maita’ A Adamawa

Related

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi
Labarai

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

20 minutes ago
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya
Labarai

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

1 hour ago
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana
Labarai

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

9 hours ago
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
Labarai

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

10 hours ago
Shettima
Labarai

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

11 hours ago
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 
Labarai

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

12 hours ago
Next Post
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

An Kama Mutane 2 Da Laifin Kashe Wani Mutum Kan 'Maita' A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.