• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Matashi Daurin Rai Da Rai Kan Yi Wa Kurma Fyade A Kebbi

by Umar Faruk
1 year ago
Fyade

Babbar kotun Jihar Kebbi, mai lamba shida a karkashin jagorancin Mai shari’a Maryam Abubakar- Kaoje, ta yanke wa wani matashi mai suna Jamilu Abdullahi da ke kauyen Dan-Warai a Karamar Hukumar Aliero hukuncin daurin rai da rai kan yi wa wata yarinya ‘yar shekara takwas da haihuwa a duniya fyade wanda yarinyar kurma ce.

Lauyan masu shigar da kara, Barista Zainab Jabbo, a nata jawabin, ta ce wanda ake tuhumar mai shekaru 13 yana fuskantar tuhuma guda daya ne kan aikata laifin fyade.

  • ‘Yan Fashi Sun Kashe Wani Dan Kasuwa A Bayelsa
  • Wasu A NNPC Ba Su So Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Kare – Sarki Sanusi

Ya aikata laifin ne a ranar 19 ga Watan Junairun 2023 a kauyen Dan-Warai da ke karamar hukumar Aliero a jihar.

“Wadda ta roki kotun da ta yanke wa wanda ake tuhumar hukuncin da ya kama ta bisa dokar da ake tuhumarsa a kai, wanda ya yaudare ta zuwa wani gini da ba a kammala ba, inda ya yi mata fyade ta hanyar sanya zakarinsa cikin farginta ba tare da yardata ba,” in ji ta.

Barista Zainab Jabbo ta roki kotu da ta hukunta wanda ake tuhuma, saboda doka ta sanya hukuncin kan tilas.

LABARAI MASU NASABA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

Laifin fyaden yana da hukunci a karkashin sashe na 210 na dokar Penal Code na Jihar Kebbi na 2021.

Mai gabatar da kara ta kira da kuma gabatar da shaidu biyar, sannan ta gabatar da takardu kara shaida na tabbatar da cewa wanda ake tuhumar ya aikata laifin.

A nasa bangaren, lauyan da ke ba da kariya ga wanda ake tuhumar a gaban kotun, Barista Bashar Zakari, ya kira wanda ake tuhumar da ya bayar da shaida domin kare kansa a gaban kotun.

Haka kuma lauyan ya roki kotun da ta yi wa wanda ake kara adalci a lokacin da za ta yanke hukuncinta.

A cikin hukuncin kotun, Mai Shari’a Maryam Abubakar-Kaoje, ta bayyana cewa kotun ta samu wanda ake kara da laifin aikata laifin fyade.

Kotun ta ce masu gabatar da kara sun tabbatar da duk abubuwan da ke nuna cewa ya aikita laifin da ake tuhumarsa.

Mai shari’a Maryam Kaoje, yayin da ta bayyana laifin a matsayin “mummuna”, ta kuma bayyana cewa wanda ake tuhumar ya yi amfani da rauninta wadda aka yi wa fyaden kuma ya ci amanar yarinyar ta hanyar aikata laifin fyaden.

“Bayan an same ka da laifin da ake tuhumarka da shi a gaban wannan kotun, kotu ta yanke maka hukuncin daurin rai da rai saboda samunka da laifin lalata wata yarinya ‘yar shekara takwas da ke zaune a garin Dan-Warai a Karamar Hukumar Aliero a Jihar ta Kebbi wanda ka aikata tun a ranar 19 ga Watan Janairu shekarar 2023.

“Wannan hukuncin zai hana wasu da za su yi tunanin aikata irin wannan laifi,” in ji ta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista
Labarai

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai
Manyan Labarai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Next Post
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

An Kama Mutane 2 Da Laifin Kashe Wani Mutum Kan 'Maita' A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.