ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Matashi Daurin Rai Da Rai Kan Yi Wa Kurma Fyade A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
Fyade

Babbar kotun Jihar Kebbi, mai lamba shida a karkashin jagorancin Mai shari’a Maryam Abubakar- Kaoje, ta yanke wa wani matashi mai suna Jamilu Abdullahi da ke kauyen Dan-Warai a Karamar Hukumar Aliero hukuncin daurin rai da rai kan yi wa wata yarinya ‘yar shekara takwas da haihuwa a duniya fyade wanda yarinyar kurma ce.

Lauyan masu shigar da kara, Barista Zainab Jabbo, a nata jawabin, ta ce wanda ake tuhumar mai shekaru 13 yana fuskantar tuhuma guda daya ne kan aikata laifin fyade.

  • ‘Yan Fashi Sun Kashe Wani Dan Kasuwa A Bayelsa
  • Wasu A NNPC Ba Su So Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Kare – Sarki Sanusi

Ya aikata laifin ne a ranar 19 ga Watan Junairun 2023 a kauyen Dan-Warai da ke karamar hukumar Aliero a jihar.

ADVERTISEMENT

“Wadda ta roki kotun da ta yanke wa wanda ake tuhumar hukuncin da ya kama ta bisa dokar da ake tuhumarsa a kai, wanda ya yaudare ta zuwa wani gini da ba a kammala ba, inda ya yi mata fyade ta hanyar sanya zakarinsa cikin farginta ba tare da yardata ba,” in ji ta.

Barista Zainab Jabbo ta roki kotu da ta hukunta wanda ake tuhuma, saboda doka ta sanya hukuncin kan tilas.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Laifin fyaden yana da hukunci a karkashin sashe na 210 na dokar Penal Code na Jihar Kebbi na 2021.

Mai gabatar da kara ta kira da kuma gabatar da shaidu biyar, sannan ta gabatar da takardu kara shaida na tabbatar da cewa wanda ake tuhumar ya aikata laifin.

A nasa bangaren, lauyan da ke ba da kariya ga wanda ake tuhumar a gaban kotun, Barista Bashar Zakari, ya kira wanda ake tuhumar da ya bayar da shaida domin kare kansa a gaban kotun.

Haka kuma lauyan ya roki kotun da ta yi wa wanda ake kara adalci a lokacin da za ta yanke hukuncinta.

A cikin hukuncin kotun, Mai Shari’a Maryam Abubakar-Kaoje, ta bayyana cewa kotun ta samu wanda ake kara da laifin aikata laifin fyade.

Kotun ta ce masu gabatar da kara sun tabbatar da duk abubuwan da ke nuna cewa ya aikita laifin da ake tuhumarsa.

Mai shari’a Maryam Kaoje, yayin da ta bayyana laifin a matsayin “mummuna”, ta kuma bayyana cewa wanda ake tuhumar ya yi amfani da rauninta wadda aka yi wa fyaden kuma ya ci amanar yarinyar ta hanyar aikata laifin fyaden.

“Bayan an same ka da laifin da ake tuhumarka da shi a gaban wannan kotun, kotu ta yanke maka hukuncin daurin rai da rai saboda samunka da laifin lalata wata yarinya ‘yar shekara takwas da ke zaune a garin Dan-Warai a Karamar Hukumar Aliero a Jihar ta Kebbi wanda ka aikata tun a ranar 19 ga Watan Janairu shekarar 2023.

“Wannan hukuncin zai hana wasu da za su yi tunanin aikata irin wannan laifi,” in ji ta.

Fyade
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

An Kama Mutane 2 Da Laifin Kashe Wani Mutum Kan 'Maita' A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.