ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Matashi Daurin Rai Da Rai Kan Yi Wa Kurma Fyade A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
Fyade

Babbar kotun Jihar Kebbi, mai lamba shida a karkashin jagorancin Mai shari’a Maryam Abubakar- Kaoje, ta yanke wa wani matashi mai suna Jamilu Abdullahi da ke kauyen Dan-Warai a Karamar Hukumar Aliero hukuncin daurin rai da rai kan yi wa wata yarinya ‘yar shekara takwas da haihuwa a duniya fyade wanda yarinyar kurma ce.

Lauyan masu shigar da kara, Barista Zainab Jabbo, a nata jawabin, ta ce wanda ake tuhumar mai shekaru 13 yana fuskantar tuhuma guda daya ne kan aikata laifin fyade.

  • ‘Yan Fashi Sun Kashe Wani Dan Kasuwa A Bayelsa
  • Wasu A NNPC Ba Su So Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Kare – Sarki Sanusi

Ya aikata laifin ne a ranar 19 ga Watan Junairun 2023 a kauyen Dan-Warai da ke karamar hukumar Aliero a jihar.

ADVERTISEMENT

“Wadda ta roki kotun da ta yanke wa wanda ake tuhumar hukuncin da ya kama ta bisa dokar da ake tuhumarsa a kai, wanda ya yaudare ta zuwa wani gini da ba a kammala ba, inda ya yi mata fyade ta hanyar sanya zakarinsa cikin farginta ba tare da yardata ba,” in ji ta.

Barista Zainab Jabbo ta roki kotu da ta hukunta wanda ake tuhuma, saboda doka ta sanya hukuncin kan tilas.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Laifin fyaden yana da hukunci a karkashin sashe na 210 na dokar Penal Code na Jihar Kebbi na 2021.

Mai gabatar da kara ta kira da kuma gabatar da shaidu biyar, sannan ta gabatar da takardu kara shaida na tabbatar da cewa wanda ake tuhumar ya aikata laifin.

A nasa bangaren, lauyan da ke ba da kariya ga wanda ake tuhumar a gaban kotun, Barista Bashar Zakari, ya kira wanda ake tuhumar da ya bayar da shaida domin kare kansa a gaban kotun.

Haka kuma lauyan ya roki kotun da ta yi wa wanda ake kara adalci a lokacin da za ta yanke hukuncinta.

A cikin hukuncin kotun, Mai Shari’a Maryam Abubakar-Kaoje, ta bayyana cewa kotun ta samu wanda ake kara da laifin aikata laifin fyade.

Kotun ta ce masu gabatar da kara sun tabbatar da duk abubuwan da ke nuna cewa ya aikita laifin da ake tuhumarsa.

Mai shari’a Maryam Kaoje, yayin da ta bayyana laifin a matsayin “mummuna”, ta kuma bayyana cewa wanda ake tuhumar ya yi amfani da rauninta wadda aka yi wa fyaden kuma ya ci amanar yarinyar ta hanyar aikata laifin fyaden.

“Bayan an same ka da laifin da ake tuhumarka da shi a gaban wannan kotun, kotu ta yanke maka hukuncin daurin rai da rai saboda samunka da laifin lalata wata yarinya ‘yar shekara takwas da ke zaune a garin Dan-Warai a Karamar Hukumar Aliero a Jihar ta Kebbi wanda ka aikata tun a ranar 19 ga Watan Janairu shekarar 2023.

“Wannan hukuncin zai hana wasu da za su yi tunanin aikata irin wannan laifi,” in ji ta.

Fyade
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

An Kama Mutane 2 Da Laifin Kashe Wani Mutum Kan 'Maita' A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.