• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Yi Wa Yara Sama da Miliyan 10 Rijistar Haihuwa Cikin Watanni 3 A Nijeriya

by Sadiq
9 months ago
Haihuwa

Hukumar Kula da Yawan Jama’a ta Nijeriya (NPC), ta sanar da cewa ta yi wa yara sama da miliyan 10 rijistar haihuwa cikin watanni uku da suka gabata. 

Wannan ci gaba ya nuna yadda ake karɓar shirin rijistar haihuwa a ƙasar, wadda ita ce mafi yawan jama’a a Afrika.

  • NLC Ta Buƙaci Gwamnatin Tinubu Ta Soke Sabuwar Dokar Haraji
  • 2025: Tinubu Ya Yi Alƙawarin Sauƙaƙa Tsadar Kayan Abinci Da Magunguna

Shugaban hukumar, Alhaji Nasir Isa Kwara, ya bayyana wannan alƙaluma yayin wani taron manema labarai da aka gudanar bayan ziyarar mai ɗakin shugaban ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, wadda ta karrama jaririn farko da aka haifa a shekarar 2025 a asibitin Asokoro, a Abuja.

Shugaban ya ce an samu karɓuwar rijistar haihuwa sosai a sassan Nijeriya.

Da yake wakiltar shugaban hukumar, kwamishinan ayyuka na Jihar Katsina, Bala Banya, ya ce NPC na aiki tuƙuru domin tabbatar da cewa duk wani jariri an yi masa rijista a ko ina yake a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Ya ƙara da cewa haɗin gwiwar da aka yi da asibitocin kula da lafiya a matakin farko da kuma amfani da sabon tsarin zamani ya taimaka sosai wajen samun wannan ci gaba.

A cewar Bala Banya, rijistar da aka yi ta haɗa da sabbin haihuwa da kuma yara ƙanana ‘yan ƙasa da shekaru biyar waɗanda ba a yi musu rijista a lokacin haihuwarsu ba.

Ya ce yanzu NPC ta fi mayar da hankali kan waɗannan yara domin cike giɓin rijistar.

A baya, babban daraktan hukumar, Dokts Telson Osifo Ojogun, ya sanar da cewa an shirya kafa cibiyoyin rijistar jarirai sama da 4,000 a faɗin ƙasar don sauƙaƙa aikin rijistar haihuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Next Post
Yadda Jawabin Shugaba Xi Ya Fayyace Manyan Nasarorin Da Sin Ta Samu A 2024

Yadda Jawabin Shugaba Xi Ya Fayyace Manyan Nasarorin Da Sin Ta Samu A 2024

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.