ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jawabin Shugaba Xi Ya Fayyace Manyan Nasarorin Da Sin Ta Samu A 2024

by Sulaiman
2 years ago
Xi

Lokaci bako! Kamar yau muka yi bankwana da shekarar 2023, ga shi a wannan karon muna bankwana da 2024 tare da murnar shigowar 2025.

Dama-dama a ce, sauran al’ummatai da shugabanninta za su yi koyi da al’ummar Sinawa da shugabanninta musamman na Afirka, wajen himma da jajircewa da za ta kai ga samun sauye-sauye da nasarori a nahiyar kamar yadda al’ummar Sinawa da shugabanninta ke da himma wajen kawo sauyi domin samun nasara a kasarsu da duniya baki daya.

  • Fargabar Hare-Haren Bello Turji Ta Tilasta Mutane Tserewa Daga Yankunan Sakkwato
  • Dokar Haraji Za Ta Ƙara Jefa Al’umma Cikin Talauci – Gwamnatin Kano

A ranar jajibirin shekarar nan ta 2025 ne, shugaban kasar Sin, Xi Jinping ya yi jawabin maraba da sabuwar shekara ta kafar yada labarai ta CMG, inda ya zayyano wasu muhimman ayyuka da kasarsa ta samu nasarori a kan su, kuma duk a cikin shekarar 2024, wannan ya cancanci yabo kuma ya zama abin fata da koyi ga sauran shugabannin duniya musamman na Afirka.

ADVERTISEMENT

Shugaba Xi Jinping ya bayyana yadda Sin ke cin moriyar amfani da cikakkun tsare-tsare na manufofi don samun ci gaba mai karfi da juriya da hakan ya haifar nasarori.

Tattalin arzikin Sin ya habbaka sosai, inda ake sa ran ma’aunin tattalin arzikin (GDP) kasar zai wuce yuan tiriliyan 130. Yawan hatsi ya haura tan miliyan 700, sannan kuma rumbunan ajiyar abincin kasar cike yake da hatsi wanda mafi yawanci girbin kasar ne (Hatsin Sinawa).

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

A karon farko, kasar Sin ta kera sabbin motoci masu amfani da makamashin lantarki fiye da miliyan 10 a cikin shekara guda. Haka kuma, a karo na farko na’urar bincike ta Chang’e 6 ta tattaro samfurori daga duniyar wata a yanki mai nisa, kana babban jirgin ruwan binciken teku na Mengxiang ya gudanar da bincike a sashen teku mai zurfi, kuma hanyar da ta ratsa teku mai hada biranen Shenzhen da Zhongshan na taimakawa ga saukaka harkokin sufuri, kuma an kara raya tashar bincike ta Qinling dake yankin Antaktika, al’amuran da suka shaida babban buri, gami da kwazon Sinawa na raya harkokin da suka shafi sararin samaniya da teku.

Bugu da kari, a cikin shekarar 2024, ’yan wasan kasar Sin sun nuna bajinta a gasar Olympics da aka gudanar a birnin Paris, lamarin da ya nuna yadda Sinawa ke cike da himma da kwarin gwiwa na kiyaye kimar kasarsu. Rundunonin sojin ruwa, da na sama na kasar Sin sun yi bukukuwan murnar cika shekaru 75 da kafuwa. Kai! Wani lamari ma mai cike da sha’awa da ban mamaki shi ne, lokacin da ambaliyar ruwa da guguwa da sauran bala’o’i suka afku a kasar, mambobin jam’iyyar kwaminis mai mulki ta kasar da jami’ai sun tashi tsaye wajen jagorantar ayyukan bayar da agajin gaggawa. Lallai wannan ya nuna cewa, Sinawa “tsintsiya daya ce madauri daya”, kuma a kowanne fanni suna aiki tukuru don cika burinsu.

Kasar Sin a matsayinta na babbar kasa mai cike da tattalin arziki. Tana kan gaba wajen ganin an yi gyare-gyare a harkokin mulkin duniya domin ganin cewa, an tafi da kowa da kowa ta hanyar zurfafa hadin kai da hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, bisa shawarar “hanya daya da ziri daya”, da tsarin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka (FOCAC), BRICS, APEC da G20.

Kasar Sin na samun nasarori ta bangaren hadin gwiwar ci gaba a tsakanin kasashe, inda take ci gaba da taka rawa wajen bai wa duniya zaman lafiya.

 

Xi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Next Post
Ɓaraka:, Ƴan Adawa, Shugabannin APC Na Shirya Kafa Sabuwar Tafiya — Lukman

Ɓaraka:, Ƴan Adawa, Shugabannin APC Na Shirya Kafa Sabuwar Tafiya — Lukman

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.