ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Jawabin Shugaba Xi Ya Fayyace Manyan Nasarorin Da Sin Ta Samu A 2024

by Sulaiman
2 years ago
Xi

Lokaci bako! Kamar yau muka yi bankwana da shekarar 2023, ga shi a wannan karon muna bankwana da 2024 tare da murnar shigowar 2025.

Dama-dama a ce, sauran al’ummatai da shugabanninta za su yi koyi da al’ummar Sinawa da shugabanninta musamman na Afirka, wajen himma da jajircewa da za ta kai ga samun sauye-sauye da nasarori a nahiyar kamar yadda al’ummar Sinawa da shugabanninta ke da himma wajen kawo sauyi domin samun nasara a kasarsu da duniya baki daya.

  • Fargabar Hare-Haren Bello Turji Ta Tilasta Mutane Tserewa Daga Yankunan Sakkwato
  • Dokar Haraji Za Ta Ƙara Jefa Al’umma Cikin Talauci – Gwamnatin Kano

A ranar jajibirin shekarar nan ta 2025 ne, shugaban kasar Sin, Xi Jinping ya yi jawabin maraba da sabuwar shekara ta kafar yada labarai ta CMG, inda ya zayyano wasu muhimman ayyuka da kasarsa ta samu nasarori a kan su, kuma duk a cikin shekarar 2024, wannan ya cancanci yabo kuma ya zama abin fata da koyi ga sauran shugabannin duniya musamman na Afirka.

ADVERTISEMENT

Shugaba Xi Jinping ya bayyana yadda Sin ke cin moriyar amfani da cikakkun tsare-tsare na manufofi don samun ci gaba mai karfi da juriya da hakan ya haifar nasarori.

Tattalin arzikin Sin ya habbaka sosai, inda ake sa ran ma’aunin tattalin arzikin (GDP) kasar zai wuce yuan tiriliyan 130. Yawan hatsi ya haura tan miliyan 700, sannan kuma rumbunan ajiyar abincin kasar cike yake da hatsi wanda mafi yawanci girbin kasar ne (Hatsin Sinawa).

LABARAI MASU NASABA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

A karon farko, kasar Sin ta kera sabbin motoci masu amfani da makamashin lantarki fiye da miliyan 10 a cikin shekara guda. Haka kuma, a karo na farko na’urar bincike ta Chang’e 6 ta tattaro samfurori daga duniyar wata a yanki mai nisa, kana babban jirgin ruwan binciken teku na Mengxiang ya gudanar da bincike a sashen teku mai zurfi, kuma hanyar da ta ratsa teku mai hada biranen Shenzhen da Zhongshan na taimakawa ga saukaka harkokin sufuri, kuma an kara raya tashar bincike ta Qinling dake yankin Antaktika, al’amuran da suka shaida babban buri, gami da kwazon Sinawa na raya harkokin da suka shafi sararin samaniya da teku.

Bugu da kari, a cikin shekarar 2024, ’yan wasan kasar Sin sun nuna bajinta a gasar Olympics da aka gudanar a birnin Paris, lamarin da ya nuna yadda Sinawa ke cike da himma da kwarin gwiwa na kiyaye kimar kasarsu. Rundunonin sojin ruwa, da na sama na kasar Sin sun yi bukukuwan murnar cika shekaru 75 da kafuwa. Kai! Wani lamari ma mai cike da sha’awa da ban mamaki shi ne, lokacin da ambaliyar ruwa da guguwa da sauran bala’o’i suka afku a kasar, mambobin jam’iyyar kwaminis mai mulki ta kasar da jami’ai sun tashi tsaye wajen jagorantar ayyukan bayar da agajin gaggawa. Lallai wannan ya nuna cewa, Sinawa “tsintsiya daya ce madauri daya”, kuma a kowanne fanni suna aiki tukuru don cika burinsu.

Kasar Sin a matsayinta na babbar kasa mai cike da tattalin arziki. Tana kan gaba wajen ganin an yi gyare-gyare a harkokin mulkin duniya domin ganin cewa, an tafi da kowa da kowa ta hanyar zurfafa hadin kai da hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa, bisa shawarar “hanya daya da ziri daya”, da tsarin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka (FOCAC), BRICS, APEC da G20.

Kasar Sin na samun nasarori ta bangaren hadin gwiwar ci gaba a tsakanin kasashe, inda take ci gaba da taka rawa wajen bai wa duniya zaman lafiya.

 

Xi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta
Ra'ayi Riga

Taswirar Duniya Mai Adalci: Afirka Ta Ki A Sake “Rage” Girmanta

September 8, 2026
Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Duk Runtsi, Akwai Mai Ba Da Kulawa Ta Musamman A Kasar Sin

September 4, 2026
Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa
Ra'ayi Riga

Samun Rarar Kudin Ciniki Ba “Laifi” Ba Ne, Hadin Gwiwa Da Cin Moriya Tare Ita Ce Mafita Ga Kowa

September 2, 2026
Next Post
Ɓaraka:, Ƴan Adawa, Shugabannin APC Na Shirya Kafa Sabuwar Tafiya — Lukman

Ɓaraka:, Ƴan Adawa, Shugabannin APC Na Shirya Kafa Sabuwar Tafiya — Lukman

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.