• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ci Gaba Da Cacar Baki Tsakanin ‘Yan Takara Da Magoya Baya Kan Kalaman Atiku

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ana Ci Gaba Da Cacar Baki Tsakanin ‘Yan Takara Da Magoya Baya Kan Kalaman Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar yana ci gaba da fuskantar matsinlamba kan kalamunsa game da dan takarar shugaban kasa da ‘yan arewa za su zaba a 2023.

Sai dai jam’iyyar APC da dan takarar shugabanta, Bola Ahmed Tinubu da sauran ‘yan Nijeriya na ci gaba da mayar da martani kan kalamun da Atiku ya yi a gaban dattawan arewa da ya gudana a Kaduna a ranar Asabar da ta gabata, inda ya kada baki ya ce ‘yan arewa ba sa bukatar shugaban kasa Bayarbe ko Ibo. A cewarsa, ‘yan arewa suna bukatar shugaban kasa da ya fito daga arewa.

  • Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau

Da yake mayar da martani dangane da kalamun Atiku, Tinubu ya bayyana cewa bai kamata tsohon mataimakin shugaban kasa ya yi magana kan shugaban kasa da ‘yan arewa za su zaba ba, inda ya ce irin wannan kalamai za su iya kawo rarrabuwar kawuna a tsakanin ‘yan Nijeriya tare da janyo kiyayya idan har aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Tinubu ya bayyana hakan ne ta bakin masu magana da yawunsa guda biyu wadanda suka hada da Cif Femi Fani-Kayode da kuma Bayo Onanuga.

Fani-Kayode wanda ya kasance tsohon ministan jiragen sama wanda a yanzu shi ne darakta yada labarai na musamman a kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na Tinubu/Shettima, ya ce abun da ‘yan Nijeriya kawai suke bukata shi ne, shugaban kasan Nijeriya ba wai shugaban arewa ba.
A bayanin da ya yi a garin Abuja, Fani-Kayode ya ce Atiku yana kokarin yin amfani da yanki, kabilanci da kuma addini.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Ya ce, “Nijeriya na bukatar ci gaba ne kadai. Kasarmu ba za ta taba amincewa da bambancin kabila ko yanki wajen zaben shugaban kasa ba. Atiku ya yi wannan magana ne a makance saboda yana gaban dimbin magoya bayan PDP.

“Nijeriya ba ta bukatar shugaban kasa dan arewa ko dan kudu, muna bukatar samun jajirtaccen shugaban kasa kamar Bola Ahmed Tinubu.”
Fani-Kayode ya kara da cewa mafi yawancin ‘yan arewa ba sa tare da Atiku wajen bambanta tsakanin arewa da kudu, domin duka daya suke. Ya ce ba za su taba barin Atiku ya yi mana irin cin amanan da ya yi wa Wike ba.

A nasa bangaren, daktan yada labaran na kawamitin yakin neman zaben shugaban kasa na Tinubu-Shettima, Bayo Onanuga ya bayyana cewa Atiku ya nuna akidarsa karara na kokarin amfani da kabilanci da yanki wanda bai kamata ya kasance haka ba a matsayinsa na tsohon shugaban kasan Nijeriya.

Onanuga ya ce, “Wannan ya nuna yadda mutumin da ya taba rike mukami na biyu a Nijeriya kuma yanzu yake kokarin a zabe shi a matsayin shugaban kasa ya rika irin wannan kalamai marasa dadin ji.

“Ya tabbata cewa Atiku idan ya samu shugabancin Nijeriya zai rarraba kawunan ‘yan Nijeriya wanda kuma hakan bai kamata ba. A yanzu haka ‘yan Nijeriya sun san wanda ya dace su zabe a matsayin shugaban kasa ba mai kokarin kawo rabuwar kai ba a tsakanin ‘yan kasa.

“Ya kamata ‘yan Nijeriya su yi watsi da Atiku a zaben da za a gudanar a watan Fabrairun 2023, domin kasarmu tana bukatar samun hadin kai ne ba rarrabuwar kawuna ba.”
A bangaren shugabancin APC kuwa, sun bayyana cewa Atiku zai wargaza hadin kan Nijeriya da kawo rudani a zaben shugaban kasa a 2023.

A cikin bayanan sakataren jam’iyyar APC na kasa, Felid Morka, ya bayyana cewa kalamun Atiku na iya tarwatsa hadin kan kasa.

Morka ya ce, “Wannan kalamai na Atiku farmaki ne ga hadin kan kasa. Bai kamata wanda ya taba rike mukamin mataimakin shugaban kasan Nijeriya a same shi yana furta irin wadannan kalamai da za su iya tarwatsa hadin kan Nijeriya domin neman samun bukatun kansa.

“Amma mu ba mu yi mamakin hakan ba domin ya nuna gazawarsa a fili na rashin iya rike mukamin shugaban kasa. Idan Atiku yana tunanin ‘yan arewa na bukatan shugaban kasa daga arewa bayan dan arewa ya kammala wa’adin mulkinsa, to yaushe ne ba a bukatar shugaban kasa dan arewa? Abin da Atiku yake tunani shi matanen kudu suke bukata a kudu.

Me ya sa ba zai yi tunanin abin da Nijeriya ke bukata ba?
“’Yan Nijeriya suna bukatar shugabanci mai ingance da zai kawo samun hadin kai a tsakanin kabilu da kuma sauran yankunan Nijeriya gaba daya. Tabbas Atiku bai cancanci zama shugaban kasa ba, domin ba zai iya gudanar da aikin hada kan ‘yan Nijeriya ba.

A yanzu kasarmu ba ta bukatar irin wadannan kalamai.”
Jam’iyyar APC ta kara da cewa wannan kalamu na Atiku su ne masu ruguza kasa cikin gaggawa maimakon samun hadin kan kasa da Nijeriya ke bukata.

Shi ma a nasa bangaren, tsohon dan takarar shugaban kasa, Farfesa Kingsley Moghalu ya bukaci Atiku ya nemi afuwan ‘yan Nijeriya.
Moghalu wanda ya yi magana a shafinsa na Tuwita da ya bayyana cewa ya yi matukar rashin jin dadinsa dangane da kalamun tsohon mataimakin shugaban kasa wanda har yanzu yana girmama shi.

Mataimaki na musamman kan yada labarai a ofishin mataimakin shugaban kasa, Louis Odion ya bayyana cewa kalamun Atiku na iya lalata hadin kan Nijeriya gaba daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Jumu’a

Next Post

Sin Dake Bin Hanyar Samun Bunkasuwa Cikin Lumana Wata Dama Ce Ga Duniya

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 week ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Sin Dake Bin Hanyar Samun Bunkasuwa Cikin Lumana Wata Dama Ce Ga Duniya

Sin Dake Bin Hanyar Samun Bunkasuwa Cikin Lumana Wata Dama Ce Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.