• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ci Gaba Da Cacar Baki Tsakanin ‘Yan Takara Da Magoya Baya Kan Kalaman Atiku

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Ana Ci Gaba Da Cacar Baki Tsakanin ‘Yan Takara Da Magoya Baya Kan Kalaman Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan takarar shugaban kasa a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar yana ci gaba da fuskantar matsinlamba kan kalamunsa game da dan takarar shugaban kasa da ‘yan arewa za su zaba a 2023.

Sai dai jam’iyyar APC da dan takarar shugabanta, Bola Ahmed Tinubu da sauran ‘yan Nijeriya na ci gaba da mayar da martani kan kalamun da Atiku ya yi a gaban dattawan arewa da ya gudana a Kaduna a ranar Asabar da ta gabata, inda ya kada baki ya ce ‘yan arewa ba sa bukatar shugaban kasa Bayarbe ko Ibo. A cewarsa, ‘yan arewa suna bukatar shugaban kasa da ya fito daga arewa.

  • Za A Iya Fuskantar Yunwa Sakamakon Ambaliyar Ruwa – Sarkin Zazzau

Da yake mayar da martani dangane da kalamun Atiku, Tinubu ya bayyana cewa bai kamata tsohon mataimakin shugaban kasa ya yi magana kan shugaban kasa da ‘yan arewa za su zaba ba, inda ya ce irin wannan kalamai za su iya kawo rarrabuwar kawuna a tsakanin ‘yan Nijeriya tare da janyo kiyayya idan har aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Tinubu ya bayyana hakan ne ta bakin masu magana da yawunsa guda biyu wadanda suka hada da Cif Femi Fani-Kayode da kuma Bayo Onanuga.

Fani-Kayode wanda ya kasance tsohon ministan jiragen sama wanda a yanzu shi ne darakta yada labarai na musamman a kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na Tinubu/Shettima, ya ce abun da ‘yan Nijeriya kawai suke bukata shi ne, shugaban kasan Nijeriya ba wai shugaban arewa ba.
A bayanin da ya yi a garin Abuja, Fani-Kayode ya ce Atiku yana kokarin yin amfani da yanki, kabilanci da kuma addini.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

Ya ce, “Nijeriya na bukatar ci gaba ne kadai. Kasarmu ba za ta taba amincewa da bambancin kabila ko yanki wajen zaben shugaban kasa ba. Atiku ya yi wannan magana ne a makance saboda yana gaban dimbin magoya bayan PDP.

“Nijeriya ba ta bukatar shugaban kasa dan arewa ko dan kudu, muna bukatar samun jajirtaccen shugaban kasa kamar Bola Ahmed Tinubu.”
Fani-Kayode ya kara da cewa mafi yawancin ‘yan arewa ba sa tare da Atiku wajen bambanta tsakanin arewa da kudu, domin duka daya suke. Ya ce ba za su taba barin Atiku ya yi mana irin cin amanan da ya yi wa Wike ba.

A nasa bangaren, daktan yada labaran na kawamitin yakin neman zaben shugaban kasa na Tinubu-Shettima, Bayo Onanuga ya bayyana cewa Atiku ya nuna akidarsa karara na kokarin amfani da kabilanci da yanki wanda bai kamata ya kasance haka ba a matsayinsa na tsohon shugaban kasan Nijeriya.

Onanuga ya ce, “Wannan ya nuna yadda mutumin da ya taba rike mukami na biyu a Nijeriya kuma yanzu yake kokarin a zabe shi a matsayin shugaban kasa ya rika irin wannan kalamai marasa dadin ji.

“Ya tabbata cewa Atiku idan ya samu shugabancin Nijeriya zai rarraba kawunan ‘yan Nijeriya wanda kuma hakan bai kamata ba. A yanzu haka ‘yan Nijeriya sun san wanda ya dace su zabe a matsayin shugaban kasa ba mai kokarin kawo rabuwar kai ba a tsakanin ‘yan kasa.

“Ya kamata ‘yan Nijeriya su yi watsi da Atiku a zaben da za a gudanar a watan Fabrairun 2023, domin kasarmu tana bukatar samun hadin kai ne ba rarrabuwar kawuna ba.”
A bangaren shugabancin APC kuwa, sun bayyana cewa Atiku zai wargaza hadin kan Nijeriya da kawo rudani a zaben shugaban kasa a 2023.

A cikin bayanan sakataren jam’iyyar APC na kasa, Felid Morka, ya bayyana cewa kalamun Atiku na iya tarwatsa hadin kan kasa.

Morka ya ce, “Wannan kalamai na Atiku farmaki ne ga hadin kan kasa. Bai kamata wanda ya taba rike mukamin mataimakin shugaban kasan Nijeriya a same shi yana furta irin wadannan kalamai da za su iya tarwatsa hadin kan Nijeriya domin neman samun bukatun kansa.

“Amma mu ba mu yi mamakin hakan ba domin ya nuna gazawarsa a fili na rashin iya rike mukamin shugaban kasa. Idan Atiku yana tunanin ‘yan arewa na bukatan shugaban kasa daga arewa bayan dan arewa ya kammala wa’adin mulkinsa, to yaushe ne ba a bukatar shugaban kasa dan arewa? Abin da Atiku yake tunani shi matanen kudu suke bukata a kudu.

Me ya sa ba zai yi tunanin abin da Nijeriya ke bukata ba?
“’Yan Nijeriya suna bukatar shugabanci mai ingance da zai kawo samun hadin kai a tsakanin kabilu da kuma sauran yankunan Nijeriya gaba daya. Tabbas Atiku bai cancanci zama shugaban kasa ba, domin ba zai iya gudanar da aikin hada kan ‘yan Nijeriya ba.

A yanzu kasarmu ba ta bukatar irin wadannan kalamai.”
Jam’iyyar APC ta kara da cewa wannan kalamu na Atiku su ne masu ruguza kasa cikin gaggawa maimakon samun hadin kan kasa da Nijeriya ke bukata.

Shi ma a nasa bangaren, tsohon dan takarar shugaban kasa, Farfesa Kingsley Moghalu ya bukaci Atiku ya nemi afuwan ‘yan Nijeriya.
Moghalu wanda ya yi magana a shafinsa na Tuwita da ya bayyana cewa ya yi matukar rashin jin dadinsa dangane da kalamun tsohon mataimakin shugaban kasa wanda har yanzu yana girmama shi.

Mataimaki na musamman kan yada labarai a ofishin mataimakin shugaban kasa, Louis Odion ya bayyana cewa kalamun Atiku na iya lalata hadin kan Nijeriya gaba daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Jumu’a

Next Post

Sin Dake Bin Hanyar Samun Bunkasuwa Cikin Lumana Wata Dama Ce Ga Duniya

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

3 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

1 week ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Sin Dake Bin Hanyar Samun Bunkasuwa Cikin Lumana Wata Dama Ce Ga Duniya

Sin Dake Bin Hanyar Samun Bunkasuwa Cikin Lumana Wata Dama Ce Ga Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.