ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Bai Wa INEC Kwanaki 7 Don Sake Nazarin Sakamakon Zaben Gwamnan Kano

by Sadiq
3 years ago
APC

Jam’iyyar APC a Jihar Kano, ta bai wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) wa’adin kwanaki bakwai don sake duba sakamakon zaben gwamnan jihar.

Leadership Hausa ta ruwaito cewa jami’in zaben Kano, Farfesa Ahmad Doko Ibrahim ya bayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben.

  • Magoya Bayan Peter Obi Sun Gudanar Da Zanga-Zanga A Abuja Kan Zaben 2023
  • Zan Yi Salon Mulki Irin Na Kwankwaso —Abba Gida-Gida

Ya jingina wannan furucin ne a kan fassarar da ya yi wa dokar zabe da kuma ka’idojin zabe cewa inda aka soke zabe sakamakon tashin hankali a kidaya tazarar shugabanci tsakanin na farko da wanda ya zo na biyu ba.

ADVERTISEMENT

Sai dai a jawabin da jam’iyyar ta yi a taron manema labarai a ranar Talata, ta bakin mai ba ta shawara kan harkokin shari’a na jihar, Barista Abdul Fagge, ta ce jami’in hukumar zabe ta INEC ya yi kurakurai tare da yin zagon kasa ga dokar zabe ta hanyar bambance soke-soke saboda tashin hankali da wuce gona da iri.

Fagge ya ce an tattara katunan zabe 273,442 a wuraren da aka soke zaben sakamakon tashin hankali da kuma yawan kuri’u, adadin da ya ce ya nuna cewa tazarar (128,897) da aka yi amfani da ita wajen bayyana Yusuf na NNPP bai wadatar ba bisa ga dokar zabe.

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Ya ce, abin mamaki ne a ce da zaben guda 16 na ‘yan majalisar dokokin da aka gudanar a rana guda kuma a karkashin sharuddan da INEC ta ce ba a kammala ba.

A nasa bangaren, Shugaban Majalisar Wakilai, Alhassan Ado Doguwa, ya ce INEC ba ta bi sharuddan da ta yi amfani da su wajen bayyana sakamakon zaben mazabarsa na tarayya a matsayin wanda bai kammala ba.

Shi ma da yake jawabi, dan takarar gwamna a jam’iyyar APC a jihar, Nasir Yusuf Gawuna, ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar da su ci gaba da kwantar da hankulan jama’a, tare da jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka yi asarar dukiyoyinsu.

Gawuna, mataimakin gwamnan jihar, ya bayyana fatansa na cewa INEC za ta yi abin da ya kamata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Next Post
CMG Da VGTRK Sun Yi Hadin Gwiwa Wajen Raya Bayanan Bidiyo Na Tarihi

CMG Da VGTRK Sun Yi Hadin Gwiwa Wajen Raya Bayanan Bidiyo Na Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.