• Leadership Hausa
Sunday, June 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Bai Wa INEC Kwanaki 7 Don Sake Nazarin Sakamakon Zaben Gwamnan Kano

by Sadiq
3 months ago
in Manyan Labarai
0
APC Ta Bai Wa INEC Kwanaki 7 Don Sake Nazarin Sakamakon Zaben Gwamnan Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar APC a Jihar Kano, ta bai wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) wa’adin kwanaki bakwai don sake duba sakamakon zaben gwamnan jihar.

Leadership Hausa ta ruwaito cewa jami’in zaben Kano, Farfesa Ahmad Doko Ibrahim ya bayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben.

  • Magoya Bayan Peter Obi Sun Gudanar Da Zanga-Zanga A Abuja Kan Zaben 2023
  • Zan Yi Salon Mulki Irin Na Kwankwaso —Abba Gida-Gida

Ya jingina wannan furucin ne a kan fassarar da ya yi wa dokar zabe da kuma ka’idojin zabe cewa inda aka soke zabe sakamakon tashin hankali a kidaya tazarar shugabanci tsakanin na farko da wanda ya zo na biyu ba.

Sai dai a jawabin da jam’iyyar ta yi a taron manema labarai a ranar Talata, ta bakin mai ba ta shawara kan harkokin shari’a na jihar, Barista Abdul Fagge, ta ce jami’in hukumar zabe ta INEC ya yi kurakurai tare da yin zagon kasa ga dokar zabe ta hanyar bambance soke-soke saboda tashin hankali da wuce gona da iri.

Fagge ya ce an tattara katunan zabe 273,442 a wuraren da aka soke zaben sakamakon tashin hankali da kuma yawan kuri’u, adadin da ya ce ya nuna cewa tazarar (128,897) da aka yi amfani da ita wajen bayyana Yusuf na NNPP bai wadatar ba bisa ga dokar zabe.

Labarai Masu Nasaba

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

Ya ce, abin mamaki ne a ce da zaben guda 16 na ‘yan majalisar dokokin da aka gudanar a rana guda kuma a karkashin sharuddan da INEC ta ce ba a kammala ba.

A nasa bangaren, Shugaban Majalisar Wakilai, Alhassan Ado Doguwa, ya ce INEC ba ta bi sharuddan da ta yi amfani da su wajen bayyana sakamakon zaben mazabarsa na tarayya a matsayin wanda bai kammala ba.

Shi ma da yake jawabi, dan takarar gwamna a jam’iyyar APC a jihar, Nasir Yusuf Gawuna, ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar da su ci gaba da kwantar da hankulan jama’a, tare da jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka yi asarar dukiyoyinsu.

Gawuna, mataimakin gwamnan jihar, ya bayyana fatansa na cewa INEC za ta yi abin da ya kamata.

Tags: Abba Kabir YusufAPCGawunaINECkanoZaben Gwamna
ShareTweetSendShare
Previous Post

Demokuradiyya Irin Na Amurka Ya Kawo Illa Ga Duniya

Next Post

CMG Da VGTRK Sun Yi Hadin Gwiwa Wajen Raya Bayanan Bidiyo Na Tarihi

Related

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano
Manyan Labarai

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

5 hours ago
Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu
Manyan Labarai

Shanun Buhari Sun Ragu Saboda Yawan Kyautarsa — Garba Shehu

11 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Zama Shugaban Kungiyar Gwamnonin PDP

1 day ago
Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano
Manyan Labarai

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

1 day ago
Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gana Da Makinde, Wike Da Ibori

2 days ago
Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur
Manyan Labarai

Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

2 days ago
Next Post
CMG Da VGTRK Sun Yi Hadin Gwiwa Wajen Raya Bayanan Bidiyo Na Tarihi

CMG Da VGTRK Sun Yi Hadin Gwiwa Wajen Raya Bayanan Bidiyo Na Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

June 4, 2023
Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

June 4, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

June 4, 2023
Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

June 4, 2023
Sana’ar Kwalliya

Sana’ar Kwalliya

June 4, 2023
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

June 4, 2023
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

June 4, 2023
Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

June 4, 2023
Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

June 4, 2023
Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

June 4, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.