ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Bai Wa INEC Kwanaki 7 Don Sake Nazarin Sakamakon Zaben Gwamnan Kano

by Sadiq
3 years ago
APC

Jam’iyyar APC a Jihar Kano, ta bai wa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) wa’adin kwanaki bakwai don sake duba sakamakon zaben gwamnan jihar.

Leadership Hausa ta ruwaito cewa jami’in zaben Kano, Farfesa Ahmad Doko Ibrahim ya bayyana Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP a matsayin wanda ya lashe zaben.

  • Magoya Bayan Peter Obi Sun Gudanar Da Zanga-Zanga A Abuja Kan Zaben 2023
  • Zan Yi Salon Mulki Irin Na Kwankwaso —Abba Gida-Gida

Ya jingina wannan furucin ne a kan fassarar da ya yi wa dokar zabe da kuma ka’idojin zabe cewa inda aka soke zabe sakamakon tashin hankali a kidaya tazarar shugabanci tsakanin na farko da wanda ya zo na biyu ba.

ADVERTISEMENT

Sai dai a jawabin da jam’iyyar ta yi a taron manema labarai a ranar Talata, ta bakin mai ba ta shawara kan harkokin shari’a na jihar, Barista Abdul Fagge, ta ce jami’in hukumar zabe ta INEC ya yi kurakurai tare da yin zagon kasa ga dokar zabe ta hanyar bambance soke-soke saboda tashin hankali da wuce gona da iri.

Fagge ya ce an tattara katunan zabe 273,442 a wuraren da aka soke zaben sakamakon tashin hankali da kuma yawan kuri’u, adadin da ya ce ya nuna cewa tazarar (128,897) da aka yi amfani da ita wajen bayyana Yusuf na NNPP bai wadatar ba bisa ga dokar zabe.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Ya ce, abin mamaki ne a ce da zaben guda 16 na ‘yan majalisar dokokin da aka gudanar a rana guda kuma a karkashin sharuddan da INEC ta ce ba a kammala ba.

A nasa bangaren, Shugaban Majalisar Wakilai, Alhassan Ado Doguwa, ya ce INEC ba ta bi sharuddan da ta yi amfani da su wajen bayyana sakamakon zaben mazabarsa na tarayya a matsayin wanda bai kammala ba.

Shi ma da yake jawabi, dan takarar gwamna a jam’iyyar APC a jihar, Nasir Yusuf Gawuna, ya yi kira ga magoya bayan jam’iyyar da su ci gaba da kwantar da hankulan jama’a, tare da jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu da kuma wadanda suka yi asarar dukiyoyinsu.

Gawuna, mataimakin gwamnan jihar, ya bayyana fatansa na cewa INEC za ta yi abin da ya kamata.

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
Manyan Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
Manyan Labarai

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Next Post
CMG Da VGTRK Sun Yi Hadin Gwiwa Wajen Raya Bayanan Bidiyo Na Tarihi

CMG Da VGTRK Sun Yi Hadin Gwiwa Wajen Raya Bayanan Bidiyo Na Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.