• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Dunkule Kan Tinubu, PDP Na Kokarin Sulhu Da Wike

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Siyasa
0
APC Ta Dunkule Kan Tinubu, PDP Na Kokarin Sulhu Da Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lokacin da aka nada gwamnan Jihar Filato, Mista Simon Lalong a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, an samu hadin kan shugabannin jam’iyyar wajen mara wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Sanata Bola Tinubu baya.

A daidai lokacin da APC ta sau nasarar hada kan ‘ya’yan jam’iyyar, ita kuma PDP ta dukufa wajen ci gaba da lallashin gwamnan Jihar Ribas, Mista Nyesom Wike, wanda ke zama babban barazana ga jam’iyyar wajen hada kan ‘ya’yanta da aka bata wa rai.

  • 2023: Peter Obi Ya Mayar Wa Da Tinubu Martani Kan Kalamansa Na Batanci A Kansa

A kokarin PDP na sulhunta ‘ya’yanta, ta kafa wani tawaga wanda gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri ya jagoranta wajen zama da tawagar gwamnan Jihar Ribas.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da wasu ‘ya’yan jam’iyyar suke bukatar shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Iyorchia Ayu ya sauka daga kan mukaminsa duk da kokarin sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar.

Nada Lalong a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na APC, mambobi da shugabannin jam’iyya mai mulki sun kulle wata baraka da ke iya jawo musu cikas a zaben 2023.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

An dai samu rashin jituwa da tayar da kura a APC saboda takarar Musulmi da Musulmi, wanda lokacin da aka nada Lalong a matsayin Daraktan Janar na yakin neman zabe dan takarar shugaban kasa na APC wasu suka yi kokarin hana shi amsa, inda ya ce ko Pope Francis ba zai hana shi amsa ba, daga baya ya bayar da hakuri lokacin da cocin katolika ta yi masa ca kan kwatanta siyasar Nijeriya da Fafaroma.

Sai dai ba a ga duriyar wasu jiga-jigan ‘yan takarar shugaban kasa kamar irin su mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo da tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi da kuma shugaban majalisan dattawa, Dakta Ahmad Lawan a wajen kaddamar da tawagar yakin neman zaman shugaban kasa na APC.

Amma kuma daraktan yada labarai na yakin neman zaben Tinubu, Mista Bayo Onanuga ya musanta rahoton da ke nuna cewa tawagar yakin neman zaben na samun turnuku. Ya kara da cewa tawagar yakin neman zaben ta hada kowa da kowa.

Onanuga ya ce Lalong shi ne ya jagoranci yakin neman zaben Amaechi da wasu gwamnoni lokacin zaben fid da gwani na jam’iyyar. Ya tabbatar da cewa tawagar ta kunshi kowa da kowa. Ya kara da cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Sanata Bola Tinubu ya sulhunta da dukkan ‘ya’yan jam’iyyar.

Onanuga ya ce, “Lalong mutumin Amaechi ne. Sannan tawagar yakin neman zabe na Osinbajo suna aiki kafada da kafada da tawagar yakin neman zaben Tinubu da Shettima. To wani kuma matsala tawagan ke fuskanta?, in ji shi.

A nasa bangaren, shugaban yakin neman zaben Osinbajo, Mista Badmus Olawale ya bayyana cewa hadin kai ne kadai zai tabbatar da samun nasarar jam’iyyar a zabe mai zuwa. Ya kara da cewa mataimakin shugaban kasa ya bukaci magoya bayansa a kan su yi biyayya ga jam’iyyar APC.

A hannu guda kuma na kokarin yin sulhu a tsakanin Wike da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, an kafa tagawa ta musamman wanda Fintiri ya jagoranta.

Tsohon ministan sadarwa, Farfesa Jerry Gana ya koka kan yadda rikicin cikin gida ke kokarin tarwasa babbar jam’iyyar adawa, inda ya nuna takaicinsa kan rashin sasanta tsohon shugaban kasa da kuma gwamnan Jihar Ribas.

A cikin mambobin kwamitin da ke bangaren Atiku akwai Fintiri da tsohon ministan harkokin ‘yansanda, Adamu Waziri da tsohon gwamnan Jihar Kuros Ribas, Sanata Liyel Imoke da tsohon dan takarar gwamna na PDP a Jihar Ondo, Mista Eyitayo Jegede (SAN) da sauran wasu mutum uku wadanda ba a ambaci sunayensu ba.

A bangaren tawagar da ke wakiltar Wike kuwa, akwai tsohon ministan shari’a, Mohammed Bello Adoke da tsohon ministan yada labarai, Gana da tsohon gwamnan Jihar Ondo, Mista Olusegun Mimiko da kuma tsohon gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Ibrahim Dankwanbo da dai sauran su.

A makon da ya gabata, PDP ta soke taron kwamitin zantarwa na jam’iyyar domin samun damar an sulhunta dukkanin ‘ya’yan jam’iyyar da aka bata wa rai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Cimma Manyan Nasarori A Fannin Gina Intanet A Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Next Post

Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

Related

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

3 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

4 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

6 days ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

7 days ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Siyasa

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

1 week ago
2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya GargaÉ—i Magoya Bayan Wike A PDP

1 week ago
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

LABARAI MASU NASABA

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi GargaÉ—i Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.