• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Dunkule Kan Tinubu, PDP Na Kokarin Sulhu Da Wike

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Siyasa
0
APC Ta Dunkule Kan Tinubu, PDP Na Kokarin Sulhu Da Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lokacin da aka nada gwamnan Jihar Filato, Mista Simon Lalong a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, an samu hadin kan shugabannin jam’iyyar wajen mara wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Sanata Bola Tinubu baya.

A daidai lokacin da APC ta sau nasarar hada kan ‘ya’yan jam’iyyar, ita kuma PDP ta dukufa wajen ci gaba da lallashin gwamnan Jihar Ribas, Mista Nyesom Wike, wanda ke zama babban barazana ga jam’iyyar wajen hada kan ‘ya’yanta da aka bata wa rai.

  • 2023: Peter Obi Ya Mayar Wa Da Tinubu Martani Kan Kalamansa Na Batanci A Kansa

A kokarin PDP na sulhunta ‘ya’yanta, ta kafa wani tawaga wanda gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri ya jagoranta wajen zama da tawagar gwamnan Jihar Ribas.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da wasu ‘ya’yan jam’iyyar suke bukatar shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Iyorchia Ayu ya sauka daga kan mukaminsa duk da kokarin sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar.

Nada Lalong a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na APC, mambobi da shugabannin jam’iyya mai mulki sun kulle wata baraka da ke iya jawo musu cikas a zaben 2023.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

An dai samu rashin jituwa da tayar da kura a APC saboda takarar Musulmi da Musulmi, wanda lokacin da aka nada Lalong a matsayin Daraktan Janar na yakin neman zabe dan takarar shugaban kasa na APC wasu suka yi kokarin hana shi amsa, inda ya ce ko Pope Francis ba zai hana shi amsa ba, daga baya ya bayar da hakuri lokacin da cocin katolika ta yi masa ca kan kwatanta siyasar Nijeriya da Fafaroma.

Sai dai ba a ga duriyar wasu jiga-jigan ‘yan takarar shugaban kasa kamar irin su mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo da tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi da kuma shugaban majalisan dattawa, Dakta Ahmad Lawan a wajen kaddamar da tawagar yakin neman zaman shugaban kasa na APC.

Amma kuma daraktan yada labarai na yakin neman zaben Tinubu, Mista Bayo Onanuga ya musanta rahoton da ke nuna cewa tawagar yakin neman zaben na samun turnuku. Ya kara da cewa tawagar yakin neman zaben ta hada kowa da kowa.

Onanuga ya ce Lalong shi ne ya jagoranci yakin neman zaben Amaechi da wasu gwamnoni lokacin zaben fid da gwani na jam’iyyar. Ya tabbatar da cewa tawagar ta kunshi kowa da kowa. Ya kara da cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Sanata Bola Tinubu ya sulhunta da dukkan ‘ya’yan jam’iyyar.

Onanuga ya ce, “Lalong mutumin Amaechi ne. Sannan tawagar yakin neman zabe na Osinbajo suna aiki kafada da kafada da tawagar yakin neman zaben Tinubu da Shettima. To wani kuma matsala tawagan ke fuskanta?, in ji shi.

A nasa bangaren, shugaban yakin neman zaben Osinbajo, Mista Badmus Olawale ya bayyana cewa hadin kai ne kadai zai tabbatar da samun nasarar jam’iyyar a zabe mai zuwa. Ya kara da cewa mataimakin shugaban kasa ya bukaci magoya bayansa a kan su yi biyayya ga jam’iyyar APC.

A hannu guda kuma na kokarin yin sulhu a tsakanin Wike da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, an kafa tagawa ta musamman wanda Fintiri ya jagoranta.

Tsohon ministan sadarwa, Farfesa Jerry Gana ya koka kan yadda rikicin cikin gida ke kokarin tarwasa babbar jam’iyyar adawa, inda ya nuna takaicinsa kan rashin sasanta tsohon shugaban kasa da kuma gwamnan Jihar Ribas.

A cikin mambobin kwamitin da ke bangaren Atiku akwai Fintiri da tsohon ministan harkokin ‘yansanda, Adamu Waziri da tsohon gwamnan Jihar Kuros Ribas, Sanata Liyel Imoke da tsohon dan takarar gwamna na PDP a Jihar Ondo, Mista Eyitayo Jegede (SAN) da sauran wasu mutum uku wadanda ba a ambaci sunayensu ba.

A bangaren tawagar da ke wakiltar Wike kuwa, akwai tsohon ministan shari’a, Mohammed Bello Adoke da tsohon ministan yada labarai, Gana da tsohon gwamnan Jihar Ondo, Mista Olusegun Mimiko da kuma tsohon gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Ibrahim Dankwanbo da dai sauran su.

A makon da ya gabata, PDP ta soke taron kwamitin zantarwa na jam’iyyar domin samun damar an sulhunta dukkanin ‘ya’yan jam’iyyar da aka bata wa rai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Cimma Manyan Nasarori A Fannin Gina Intanet A Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Next Post

Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

Related

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

2 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

4 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

4 days ago
Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai FaÉ—i – Shehu Sani
Manyan Labarai

Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai FaÉ—i – Shehu Sani

5 days ago
PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke
Siyasa

PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke

5 days ago
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.