• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Dunkule Kan Tinubu, PDP Na Kokarin Sulhu Da Wike

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Siyasa
0
APC Ta Dunkule Kan Tinubu, PDP Na Kokarin Sulhu Da Wike
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Lokacin da aka nada gwamnan Jihar Filato, Mista Simon Lalong a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, an samu hadin kan shugabannin jam’iyyar wajen mara wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Sanata Bola Tinubu baya.

A daidai lokacin da APC ta sau nasarar hada kan ‘ya’yan jam’iyyar, ita kuma PDP ta dukufa wajen ci gaba da lallashin gwamnan Jihar Ribas, Mista Nyesom Wike, wanda ke zama babban barazana ga jam’iyyar wajen hada kan ‘ya’yanta da aka bata wa rai.

  • 2023: Peter Obi Ya Mayar Wa Da Tinubu Martani Kan Kalamansa Na Batanci A Kansa

A kokarin PDP na sulhunta ‘ya’yanta, ta kafa wani tawaga wanda gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri ya jagoranta wajen zama da tawagar gwamnan Jihar Ribas.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da wasu ‘ya’yan jam’iyyar suke bukatar shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Iyorchia Ayu ya sauka daga kan mukaminsa duk da kokarin sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar.

Nada Lalong a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na APC, mambobi da shugabannin jam’iyya mai mulki sun kulle wata baraka da ke iya jawo musu cikas a zaben 2023.

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

An dai samu rashin jituwa da tayar da kura a APC saboda takarar Musulmi da Musulmi, wanda lokacin da aka nada Lalong a matsayin Daraktan Janar na yakin neman zabe dan takarar shugaban kasa na APC wasu suka yi kokarin hana shi amsa, inda ya ce ko Pope Francis ba zai hana shi amsa ba, daga baya ya bayar da hakuri lokacin da cocin katolika ta yi masa ca kan kwatanta siyasar Nijeriya da Fafaroma.

Sai dai ba a ga duriyar wasu jiga-jigan ‘yan takarar shugaban kasa kamar irin su mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo da tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi da kuma shugaban majalisan dattawa, Dakta Ahmad Lawan a wajen kaddamar da tawagar yakin neman zaman shugaban kasa na APC.

Amma kuma daraktan yada labarai na yakin neman zaben Tinubu, Mista Bayo Onanuga ya musanta rahoton da ke nuna cewa tawagar yakin neman zaben na samun turnuku. Ya kara da cewa tawagar yakin neman zaben ta hada kowa da kowa.

Onanuga ya ce Lalong shi ne ya jagoranci yakin neman zaben Amaechi da wasu gwamnoni lokacin zaben fid da gwani na jam’iyyar. Ya tabbatar da cewa tawagar ta kunshi kowa da kowa. Ya kara da cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Sanata Bola Tinubu ya sulhunta da dukkan ‘ya’yan jam’iyyar.

Onanuga ya ce, “Lalong mutumin Amaechi ne. Sannan tawagar yakin neman zabe na Osinbajo suna aiki kafada da kafada da tawagar yakin neman zaben Tinubu da Shettima. To wani kuma matsala tawagan ke fuskanta?, in ji shi.

A nasa bangaren, shugaban yakin neman zaben Osinbajo, Mista Badmus Olawale ya bayyana cewa hadin kai ne kadai zai tabbatar da samun nasarar jam’iyyar a zabe mai zuwa. Ya kara da cewa mataimakin shugaban kasa ya bukaci magoya bayansa a kan su yi biyayya ga jam’iyyar APC.

A hannu guda kuma na kokarin yin sulhu a tsakanin Wike da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, an kafa tagawa ta musamman wanda Fintiri ya jagoranta.

Tsohon ministan sadarwa, Farfesa Jerry Gana ya koka kan yadda rikicin cikin gida ke kokarin tarwasa babbar jam’iyyar adawa, inda ya nuna takaicinsa kan rashin sasanta tsohon shugaban kasa da kuma gwamnan Jihar Ribas.

A cikin mambobin kwamitin da ke bangaren Atiku akwai Fintiri da tsohon ministan harkokin ‘yansanda, Adamu Waziri da tsohon gwamnan Jihar Kuros Ribas, Sanata Liyel Imoke da tsohon dan takarar gwamna na PDP a Jihar Ondo, Mista Eyitayo Jegede (SAN) da sauran wasu mutum uku wadanda ba a ambaci sunayensu ba.

A bangaren tawagar da ke wakiltar Wike kuwa, akwai tsohon ministan shari’a, Mohammed Bello Adoke da tsohon ministan yada labarai, Gana da tsohon gwamnan Jihar Ondo, Mista Olusegun Mimiko da kuma tsohon gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Ibrahim Dankwanbo da dai sauran su.

A makon da ya gabata, PDP ta soke taron kwamitin zantarwa na jam’iyyar domin samun damar an sulhunta dukkanin ‘ya’yan jam’iyyar da aka bata wa rai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Cimma Manyan Nasarori A Fannin Gina Intanet A Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Next Post

Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

4 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

5 days ago
Sulhun PDP Ya HaÉ—u Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya HaÉ—u Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

1 week ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.