ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

by Aisha Seyoji
4 years ago
Kayan masarufi

Barkanmu da sake saduwa daku a wannan filin namu, a wannan makon mun kawo muku ra’ayoyinku ne a kanj yadda ake samun hauhawar farashin kayan masarufi a Nijeriya, shin, yaya take ne a yankunan ku?

Yahaya Aliyu Sani
To abin dai yawuce tunanin mu sai dai mu yi ta addu’a domin ganin canji

Adam Ajiya
To ba abin da za mu ce sai innalillahi wa inna ilaihirrajiun don abin ya fi Karfin tunanin dan adam, komai Kara hawa yake, wani abinma wallahi kawai sharrin ‘yan kasuwa ne sai a fakeda shuwagabanni to Allah mun tuba ka yafe mana ka kawo mana sauKin lamurra

ADVERTISEMENT

It’z Sam Dambatta
To Babu abin da za mu ce sai dai mu yi wa Allah godiya domin kuwa a sakamakon sabonn amfanin gona ya kusa zuwa gida, wanda suka sayi abinci suka boye sun fara fito dashi a sanadiyar hakan da yawa daga cikinsu farashin ya fara raguwa sai dai fatan Allah ya sa a tafi a haka

Khadija Muhammad
Sai hamdala al’amarin ya wuce hankali domin karin ya zama kullum da safe da yamma abinda na fahimta shi ne har da mugunta irin tamu, Allah ya shiryar da mu mu daina cutar da juna

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

Idris Saminu Shuaibu
Gaskiya maganar hauhawar farashi na kayayyaki abin ba a cewa komai yau idan kana da jarin dubu 10 to gobe da ka koma kasuwa zai zama na dubu 8 ko kasa da haka kullum kaya Kara tsawwalewa suke sai dai mu yi addu’a Allah ya kawo mana dauki kuma mu gyara halayen mu

It’z Jameel Moh’d
Gaskiya a yankinmu babu sauKi kawai dai addu’a muke yi kullum Allah ya kawo mana dauki cikin sauKi, ga matsalar tsaro ga hauhawar kayan masarufi, dame talaka a wannan Kasar zai ji

Lami S Mudu
Abin sai dai godiyar Allah, amma ai maganar hauhawar kayan masarufi ruwan dare ne game duniya, muna roKon Allah ya kawo mana sauKi a cikin al’amarin ya ba mu abinda zamu tsaya akai

Fa’izah Muhammad Sajo
Abin ba a Magana, yanzu mamana ta dawo kasuwa komi ya tashi a nan kasuwar Kawo da ke Kaduna

Bashir Ibrahim Matazu
Abin sai dai addu’a, Bredin din da nake Saya 450 a 2020 Yanzu Ya koma Naira 1,000 abin sai addu’a kawai, Allah Ya hore mana abin siya, amin.

Abubakar Muhammad Kirfi
Anan Gombe babu sauKi cutar arne

Hussain SO Sartsen Zuci
Ruwan dare ne ya shafi ko ina, abin kam ba sauKi sai dai daga wajen ALLAH.

Abdulmumini Sese
Gida ya tsaya chak

Fatima Ibrahim Mukhtar
Ba sauki ko digo a nan Ikko

Adamu Yunusa Ibrahim
Bahaushe ya yi gaskiya da ya ce “Idan an bi ta barawo, sai a dawo a bi ta mai bin sawu”. Da yawa ‘Yankasuwarmu na da hannu dumu-dumu wajen hauhawar farashin kayayyakin masarufi a Arewacin Nijeriya in da na fi sani. Mutane na da mummunar dabi’ar sayen kayan amfanin gona, a lokacin girbi suna boyewa, sai ya yi tsada a fito da shi. Ko shakka babu wannan na daga cikin dalilan da ke sa wa, kayan amfanin gonar yin tashin gwauron zabo a kusan dukkansu Kasar.
Haka kuma rashin tsari mai kyau daga Gwamnati shi ma yana taka muhimmiyar rawa, wajen kawo tsadar masarufi. Yakamata Gwamnati ta yi dayan hudu.
A. Ko dai ta samar da tallafi a kan kayan masarufin ta hanyar bayar da bashi maras ruwa ga manoma, kuma idan sun noma ta saya da tsada, sannan ta karya shi a kasuwa domin Talakawa marasa Karfi su amfana. Idan aka yi haka za a samu amfani kusan biyar. Na farko dai an taimaki manoman wajen samar musu da bashin da babu ruwa. Na biyu, an sake taimakar manoman ta hanyar sayen kayan amfanin gonar da daraja. Haka kuma an taimaki marasa Karfi, domin za su samu abinci a rahusa. Hakan zai bayar da natsuwa da kwanciyar hankali a Kasa. Sannan uwa zai bunKasa tattalin arzikin Kasa, da na jama’a.
B. Idan haka ba za ta samu ba, Gwamnati ta shiga harkar noma gadan-gadan. Wato, ta nemi gonaki da za ta zuba kudi ta yi noman rani da na damuna, sannan ta rika sayar wa da Talakawa da sauKi.
C. Idan haka ba ta samu ba, Gwamnati na iya bude bodojin Kasar, ta yadda za a samu a riKa shigo da abinci daga maKwabta. Wanda hakan zai samar da gasa a tsakanin kamfanonin shigo da abinci. Idan aka samu gasa, dole za a samu sauKi. Domin idan wannan ya tsawwala, tabbas wancan zai sauKaKa. Hakan zai sa a samu sauKi.
D. Ko kuma ita Gwamnatin ta riKa shigo da abincin daga Kasar waje, tana sayarwa da Talakawa a kudi mai rahusa.
Idan aka dauki daya daga cikin wadancan matakan tabbas abinci zai wadata, kuma zai yi sauKi. Domin tsakani da Allah, mutane na cikin damuwa a kan yadda kayan masarufi ke neman gagararsu. Domin duk abin da ka saya yau a Kasuwa, gobe idan ka koma sai an Kara wani abu a kai. Babu zancen sauKi.
Comrade Adamu Yunusa Ibrahim,
Malami a Cibiyar Nazarin Hausa,
Jami’ar Usmanu Danfodiyo,
Sakkwato, Nijeriya.
SadeeK Rufa’i Banguguwa
Allah yana cewa:”ArziKinku yana sama hakanan abinda ake muku alKawari da shi”
Lalle cikin wadannan kwanaki ana fama da tsadar kayan masarufi, da hauhawar farashi musamman kuma a wannan Kasa tamu Nigeria, rayuwa tana neman ta gagari mutane da yawa.
Sai dai mu sani hakan na faruwa ne da nufin Allah, domin shi ne mai sanyawa komai farashi, kuma mai shimfida arziKi mai damKe shi, kamar yadda Annabi ya fada a cikin hadisin da Muslim ya rawaito.
don haka mu rika tunawa da wannan, mu fahimci cewa ana jin dadi ne sanda Allah ya yi nufi a sha wahala sanda yai nufi.
An ce da Ibrahim Dan Adhama: “Farashi ya tashi sai ya ce : “Idan da alkama daya za ta zama Dinare daya ake saida ita hakan ba zai dameni ba, wajibin da ke kaina na bautawa Allah kamar yadda ya umarce ni, Shi kuma zai azurtani kamar yadda ya yi alKawari” Allah ta’ala yana cewa: “Ban halicci Aljanu da Mutane ba, sai domin su bauta min, bana neman arziki daga wajensu, bana neman su ciyar da ni, lalle Allah shine mai azurtawa kuma mai karfi.
Allah ka bamu abinda za mu sayi abinda muke buKata, ka yalwata mana arzikin mu. Amman tabbas akwai matsalar hauhawar farashi a wannan lokacin, sai dai in muka mika lamarinmu ga Ubangijunmu sai ya taimakemu.
SadeeK Rufa’i Banguguwa.

Hon Hafeez KiiDo
Jiya da aka gaya min kudin man gyada kwalba daya saida na nemi inuwa na zauna. A baya har 200 na siya mai kwalba, Karshen tsadarsa ya zama 400+, amma kwatsam sai ji na yi ana cewa wai ga 1,100 a siyo mai kwalba daya. Na girgiza.
Sai dai haka yawancin abubuwa suka koma, don ko Taliya da nake siyan katan 2,200 a yanzu haka naira 7,800 nake siyanta. Haka komai ya ninka kansa sau kamar uku ko hudu. HaKiKa ana shan wahala sosai, kuma duk da haka babu Karin albashin ko sisi ga ma’aikata

Kayan masarufi
Aisha Seyoji
+ postsBio
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Ra’ayoyinku A Kan Ba Da Bashi Ga Daliban Manyan Makarantu
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
An Kama Sojoji 2 Kan Zargin Suna Da Hannu A Kisan Wani Malamin Addinin Musulunci A Yobe

An Kama Sojoji 2 Kan Zargin Suna Da Hannu A Kisan Wani Malamin Addinin Musulunci A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

Sojoji Sun Kama Mai Kai Wa Ƴan Ta’adda Kayan Aiki A Zamfara

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.