ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Dunkule Kan Tinubu, PDP Na Kokarin Sulhu Da Wike

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
APC

Lokacin da aka nada gwamnan Jihar Filato, Mista Simon Lalong a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, an samu hadin kan shugabannin jam’iyyar wajen mara wa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Sanata Bola Tinubu baya.

A daidai lokacin da APC ta sau nasarar hada kan ‘ya’yan jam’iyyar, ita kuma PDP ta dukufa wajen ci gaba da lallashin gwamnan Jihar Ribas, Mista Nyesom Wike, wanda ke zama babban barazana ga jam’iyyar wajen hada kan ‘ya’yanta da aka bata wa rai.

  • 2023: Peter Obi Ya Mayar Wa Da Tinubu Martani Kan Kalamansa Na Batanci A Kansa

A kokarin PDP na sulhunta ‘ya’yanta, ta kafa wani tawaga wanda gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Fintiri ya jagoranta wajen zama da tawagar gwamnan Jihar Ribas.

ADVERTISEMENT

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da wasu ‘ya’yan jam’iyyar suke bukatar shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Iyorchia Ayu ya sauka daga kan mukaminsa duk da kokarin sulhunta ‘ya’yan jam’iyyar.

Nada Lalong a matsayin Darakta Janar na yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na APC, mambobi da shugabannin jam’iyya mai mulki sun kulle wata baraka da ke iya jawo musu cikas a zaben 2023.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

An dai samu rashin jituwa da tayar da kura a APC saboda takarar Musulmi da Musulmi, wanda lokacin da aka nada Lalong a matsayin Daraktan Janar na yakin neman zabe dan takarar shugaban kasa na APC wasu suka yi kokarin hana shi amsa, inda ya ce ko Pope Francis ba zai hana shi amsa ba, daga baya ya bayar da hakuri lokacin da cocin katolika ta yi masa ca kan kwatanta siyasar Nijeriya da Fafaroma.

Sai dai ba a ga duriyar wasu jiga-jigan ‘yan takarar shugaban kasa kamar irin su mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo da tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi da kuma shugaban majalisan dattawa, Dakta Ahmad Lawan a wajen kaddamar da tawagar yakin neman zaman shugaban kasa na APC.

Amma kuma daraktan yada labarai na yakin neman zaben Tinubu, Mista Bayo Onanuga ya musanta rahoton da ke nuna cewa tawagar yakin neman zaben na samun turnuku. Ya kara da cewa tawagar yakin neman zaben ta hada kowa da kowa.

Onanuga ya ce Lalong shi ne ya jagoranci yakin neman zaben Amaechi da wasu gwamnoni lokacin zaben fid da gwani na jam’iyyar. Ya tabbatar da cewa tawagar ta kunshi kowa da kowa. Ya kara da cewa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Sanata Bola Tinubu ya sulhunta da dukkan ‘ya’yan jam’iyyar.

Onanuga ya ce, “Lalong mutumin Amaechi ne. Sannan tawagar yakin neman zabe na Osinbajo suna aiki kafada da kafada da tawagar yakin neman zaben Tinubu da Shettima. To wani kuma matsala tawagan ke fuskanta?, in ji shi.

A nasa bangaren, shugaban yakin neman zaben Osinbajo, Mista Badmus Olawale ya bayyana cewa hadin kai ne kadai zai tabbatar da samun nasarar jam’iyyar a zabe mai zuwa. Ya kara da cewa mataimakin shugaban kasa ya bukaci magoya bayansa a kan su yi biyayya ga jam’iyyar APC.

A hannu guda kuma na kokarin yin sulhu a tsakanin Wike da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, an kafa tagawa ta musamman wanda Fintiri ya jagoranta.

Tsohon ministan sadarwa, Farfesa Jerry Gana ya koka kan yadda rikicin cikin gida ke kokarin tarwasa babbar jam’iyyar adawa, inda ya nuna takaicinsa kan rashin sasanta tsohon shugaban kasa da kuma gwamnan Jihar Ribas.

A cikin mambobin kwamitin da ke bangaren Atiku akwai Fintiri da tsohon ministan harkokin ‘yansanda, Adamu Waziri da tsohon gwamnan Jihar Kuros Ribas, Sanata Liyel Imoke da tsohon dan takarar gwamna na PDP a Jihar Ondo, Mista Eyitayo Jegede (SAN) da sauran wasu mutum uku wadanda ba a ambaci sunayensu ba.

A bangaren tawagar da ke wakiltar Wike kuwa, akwai tsohon ministan shari’a, Mohammed Bello Adoke da tsohon ministan yada labarai, Gana da tsohon gwamnan Jihar Ondo, Mista Olusegun Mimiko da kuma tsohon gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Ibrahim Dankwanbo da dai sauran su.

A makon da ya gabata, PDP ta soke taron kwamitin zantarwa na jam’iyyar domin samun damar an sulhunta dukkanin ‘ya’yan jam’iyyar da aka bata wa rai.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Next Post
Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

Ra’ayoyinku A Kan Hauhawar Farashin Kayan Masarufi

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.