• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Kasa Cika Alƙawarin Sauya Fasalin Ƙasa, In Ji Atiku

by Sulaiman
2 years ago
in Siyasa
0
APC Ta Kasa Cika Alƙawarin Sauya Fasalin Ƙasa, In Ji Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya sake nanata ƙudirin sa na rage wa Gwamnatin Tarayya ƙarfin iko tare da sauya fasalin ƙasar nan idan ya ci zaɓe.

 

Haka kuma ya zargi jam’iyyar APC da ke mulki da cewar ta ƙi cika alƙawarin da ta yi na sauya fasalin ƙasar.

  • Ku Zarge Ni Idan Har Miji Na Ya Gaza Cika Alkawuran Da Ya Dauka Yayin Yakin Neman Zabe” -Titi Atiku

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya yi wannan maganar ne a dandalin wasa na Pa Oruta Ngele da ke Abakaliki, Jihar Ebonyi, lokacin da ya je can yaƙin neman zaɓe.

 

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Atiku ya ce ‘yan ƙabilar Ibo sun sha yin kira da a sauya fasalin ƙasa (wato ‘restructuring’ a turance) domin su magance matsalolin da ke addabar yankin su, don haka ya ce sauya fasalin ƙasa na daga cikin manyan ƙudirorin da zai sa a gaba idan ya kafa gwamnati a matsayin shugaban Nijeriya.

 

Ya yi iƙirarin cewa ita APC ta gaza wajen cika alƙawarin da ta yi na sauya fasalin ƙasa, ya ce ya na kira ga al’ummar Ibo da ke Jihar Ebonyi da su yi watsi da jam’iyyar APC a zaɓen shugaban ƙasa da za a yi.

 

Atiku ya samu babbar tarba a filin wasan inda ɗimbin jama’a su ka taru domin su saurare shi.

 

Ɗan takarar ya gode wa jama’ar jihar saboda goyon bayan da su ke ba PDP tun da aka kafa ta a cikin 1999.

 

Ya ce: “Na ƙudiri aniyar sakar wa matakan gwamnati da ke ƙasan Gwamnatin Tarayya ƙarfin iko da kuma sauya fasalin ƙasar nan; al’ummar yankin Kudu-maso-gabas sun daɗe su na ƙawazuci tare da yekuwar a sauya fasalin ƙasa saboda su na so su samu ƙarin ƙarfin iko da ƙarin kuɗi domin magance matsalolin da ke damun su.

 

“Mun amince da hakan kuma wannan ne ya sa hakan zai kasance wani babban ginshiƙi na gwamnatin mu. Saboda haka, ku ba mu goyon baya har ku ka ba mu damar zama shugaban ƙasa na gaba.”

 

Ya ƙara da cewa, “APC sun yi maku irin wannan alƙawarin. Shin amma sun yi? Sai su ka yi watsi da wannan batun na sauya fasalin ƙasa. Jam’iyyar su ta manyan ‘yan yaudara ce, kuma haɗakar su ta tantagaryar yaudara ce.

 

“Mun ƙudiri aniya kuma gaskiya ce mu ke faɗa, don haka idan ku ka ba mu goyon baya, za mu aiwatar da alƙawarin da mu ka ɗauka.”

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, zai kara da Atiku Abubakar na PDP a babban zaɓen da za a gudanar a ranar 25 ga Fabrairu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwantena Ta Latse Wata Motar Bas, Ta Kashe Fasinjoji 8 A Legas

Next Post

Sin Na Gabatar Da Kyakkyawan Misali A Fannin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa In Ji Wani Masani

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

4 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

5 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

1 week ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Sin Na Gabatar Da Kyakkyawan Misali A Fannin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa In Ji Wani Masani

Sin Na Gabatar Da Kyakkyawan Misali A Fannin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa In Ji Wani Masani

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
APC

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.