• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Kasa Cika Alƙawarin Sauya Fasalin Ƙasa, In Ji Atiku

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
APC Ta Kasa Cika Alƙawarin Sauya Fasalin Ƙasa, In Ji Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya sake nanata ƙudirin sa na rage wa Gwamnatin Tarayya ƙarfin iko tare da sauya fasalin ƙasar nan idan ya ci zaɓe.

 

Haka kuma ya zargi jam’iyyar APC da ke mulki da cewar ta ƙi cika alƙawarin da ta yi na sauya fasalin ƙasar.

  • Ku Zarge Ni Idan Har Miji Na Ya Gaza Cika Alkawuran Da Ya Dauka Yayin Yakin Neman Zabe” -Titi Atiku

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya yi wannan maganar ne a dandalin wasa na Pa Oruta Ngele da ke Abakaliki, Jihar Ebonyi, lokacin da ya je can yaƙin neman zaɓe.

 

Labarai Masu Nasaba

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

Atiku ya ce ‘yan ƙabilar Ibo sun sha yin kira da a sauya fasalin ƙasa (wato ‘restructuring’ a turance) domin su magance matsalolin da ke addabar yankin su, don haka ya ce sauya fasalin ƙasa na daga cikin manyan ƙudirorin da zai sa a gaba idan ya kafa gwamnati a matsayin shugaban Nijeriya.

 

Ya yi iƙirarin cewa ita APC ta gaza wajen cika alƙawarin da ta yi na sauya fasalin ƙasa, ya ce ya na kira ga al’ummar Ibo da ke Jihar Ebonyi da su yi watsi da jam’iyyar APC a zaɓen shugaban ƙasa da za a yi.

 

Atiku ya samu babbar tarba a filin wasan inda ɗimbin jama’a su ka taru domin su saurare shi.

 

Ɗan takarar ya gode wa jama’ar jihar saboda goyon bayan da su ke ba PDP tun da aka kafa ta a cikin 1999.

 

Ya ce: “Na ƙudiri aniyar sakar wa matakan gwamnati da ke ƙasan Gwamnatin Tarayya ƙarfin iko da kuma sauya fasalin ƙasar nan; al’ummar yankin Kudu-maso-gabas sun daɗe su na ƙawazuci tare da yekuwar a sauya fasalin ƙasa saboda su na so su samu ƙarin ƙarfin iko da ƙarin kuɗi domin magance matsalolin da ke damun su.

 

“Mun amince da hakan kuma wannan ne ya sa hakan zai kasance wani babban ginshiƙi na gwamnatin mu. Saboda haka, ku ba mu goyon baya har ku ka ba mu damar zama shugaban ƙasa na gaba.”

 

Ya ƙara da cewa, “APC sun yi maku irin wannan alƙawarin. Shin amma sun yi? Sai su ka yi watsi da wannan batun na sauya fasalin ƙasa. Jam’iyyar su ta manyan ‘yan yaudara ce, kuma haɗakar su ta tantagaryar yaudara ce.

 

“Mun ƙudiri aniya kuma gaskiya ce mu ke faɗa, don haka idan ku ka ba mu goyon baya, za mu aiwatar da alƙawarin da mu ka ɗauka.”

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, zai kara da Atiku Abubakar na PDP a babban zaɓen da za a gudanar a ranar 25 ga Fabrairu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwantena Ta Latse Wata Motar Bas, Ta Kashe Fasinjoji 8 A Legas

Next Post

Sin Na Gabatar Da Kyakkyawan Misali A Fannin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa In Ji Wani Masani

Related

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci
Siyasa

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

29 minutes ago
Labarai

Ɗaruruwan Mambobin APC Sun Sauya Sheka Zuwa ADC A Sokoto

2 days ago
Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC
Labarai

Akwai Katin Zaɓe Fiye Da Dubu 367 Da Ba A Karɓa Ba A Kano – INEC

2 days ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

4 days ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

5 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

6 days ago
Next Post
Sin Na Gabatar Da Kyakkyawan Misali A Fannin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa In Ji Wani Masani

Sin Na Gabatar Da Kyakkyawan Misali A Fannin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa In Ji Wani Masani

LABARAI MASU NASABA

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

Ɗaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.