ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Ta Kasa Cika Alƙawarin Sauya Fasalin Ƙasa, In Ji Atiku

by Sulaiman
3 years ago
APC

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya sake nanata ƙudirin sa na rage wa Gwamnatin Tarayya ƙarfin iko tare da sauya fasalin ƙasar nan idan ya ci zaɓe.

 

Haka kuma ya zargi jam’iyyar APC da ke mulki da cewar ta ƙi cika alƙawarin da ta yi na sauya fasalin ƙasar.

ADVERTISEMENT
  • Ku Zarge Ni Idan Har Miji Na Ya Gaza Cika Alkawuran Da Ya Dauka Yayin Yakin Neman Zabe” -Titi Atiku

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya yi wannan maganar ne a dandalin wasa na Pa Oruta Ngele da ke Abakaliki, Jihar Ebonyi, lokacin da ya je can yaƙin neman zaɓe.

 

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Atiku ya ce ‘yan ƙabilar Ibo sun sha yin kira da a sauya fasalin ƙasa (wato ‘restructuring’ a turance) domin su magance matsalolin da ke addabar yankin su, don haka ya ce sauya fasalin ƙasa na daga cikin manyan ƙudirorin da zai sa a gaba idan ya kafa gwamnati a matsayin shugaban Nijeriya.

 

Ya yi iƙirarin cewa ita APC ta gaza wajen cika alƙawarin da ta yi na sauya fasalin ƙasa, ya ce ya na kira ga al’ummar Ibo da ke Jihar Ebonyi da su yi watsi da jam’iyyar APC a zaɓen shugaban ƙasa da za a yi.

 

Atiku ya samu babbar tarba a filin wasan inda ɗimbin jama’a su ka taru domin su saurare shi.

 

Ɗan takarar ya gode wa jama’ar jihar saboda goyon bayan da su ke ba PDP tun da aka kafa ta a cikin 1999.

 

Ya ce: “Na ƙudiri aniyar sakar wa matakan gwamnati da ke ƙasan Gwamnatin Tarayya ƙarfin iko da kuma sauya fasalin ƙasar nan; al’ummar yankin Kudu-maso-gabas sun daɗe su na ƙawazuci tare da yekuwar a sauya fasalin ƙasa saboda su na so su samu ƙarin ƙarfin iko da ƙarin kuɗi domin magance matsalolin da ke damun su.

 

“Mun amince da hakan kuma wannan ne ya sa hakan zai kasance wani babban ginshiƙi na gwamnatin mu. Saboda haka, ku ba mu goyon baya har ku ka ba mu damar zama shugaban ƙasa na gaba.”

 

Ya ƙara da cewa, “APC sun yi maku irin wannan alƙawarin. Shin amma sun yi? Sai su ka yi watsi da wannan batun na sauya fasalin ƙasa. Jam’iyyar su ta manyan ‘yan yaudara ce, kuma haɗakar su ta tantagaryar yaudara ce.

 

“Mun ƙudiri aniya kuma gaskiya ce mu ke faɗa, don haka idan ku ka ba mu goyon baya, za mu aiwatar da alƙawarin da mu ka ɗauka.”

 

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu, zai kara da Atiku Abubakar na PDP a babban zaɓen da za a gudanar a ranar 25 ga Fabrairu.

APC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai
  • Sulaiman
    Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel
  • Sulaiman
    Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya
  • Sulaiman
    Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Next Post
Sin Na Gabatar Da Kyakkyawan Misali A Fannin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa In Ji Wani Masani

Sin Na Gabatar Da Kyakkyawan Misali A Fannin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa In Ji Wani Masani

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026
Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

Burina Zama Daya Daga Cikin Fitattun Masu Daukar Hoto A Nijeriya –Ibrahim Aminu

July 18, 2026
Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

Omar M. Yaghi: Kalaman Xi Sun Kara Mana Kwarin Gwiwa

July 18, 2026
Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

Manufar Sin Ta Ba Da Jagoranci Ga Tafiyar Da Fasahar AI A Duniya

July 18, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Wa Sin Bisa Goyon Bayanta Ga Dakile Cutar Ebola

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.