• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APEC: Nisan Wuri Ba Ya Hana Sada Zumunci Da Kulla Alheri Tsakanin Sin Da Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
APEC: Nisan Wuri Ba Ya Hana Sada Zumunci Da Kulla Alheri Tsakanin Sin Da Kasashen Duniya

LIMA, PERU - 2024/11/10: Social media Lounge view in the First day of the APEC Peru 2024 Economic Leaders Week (AELW). The Asia-Pacific Economic Cooperation (APEC), established in November 1989, is an economic forum composed of 21 Asia-Pacific economies, considered the most dynamic region in the world. (Photo by Carlos Garcia Granthon/Fotoholica Press/LightRocket via Getty Images)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun ana sauran mako guda a gudanar da taron shugabannin tattalin arzikin Kungiyar Hadin Gwiwar Asiya da Yankin Tekun Fasifik wato APEC, karo na 31, wanda aka kamala ranar 16 ga Nuwamban nan, kafofin watsa labarai na duniya suka yi ta yayata batun taron musamman a kasashen da abin ya shafa.

 

Hadin gwiwar da ya haifar da kafuwar kungiyar APEC a shekarar 1989 ya zama tamkar wani sabon-wata-sha-kallo saboda alfanun da yake tattare da shi da kuma zama wani madubi dai zai haska wa daukacin mutane masu rajin kawo sauyi da ci gaban al’ummar duniya na bai-daya irin turbar da ya dace kasashe musamman a matakin yankuna su bi domin fita daga kangin danniya da rashin makama wurin warware dabaibayin da ya hana ruwa gudu ga ci gaban tattalin arzikinsu.

  • Buhari Ya Taya APC Murna Kan Nasararta A Jihar Ondo
  • CMG Da El Comercio Group Na Kasar Peru Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zurfafa Hadin Gwiwa

Kamar yadda alkaluma suka nuna daga majiyoyi daban-daban, daga shekarar 2014 zuwa 2022, hada-hadar tattalin arzikin kasashen kungiyar ta APEC ta habaka zuwa kimanin dala tiriliyan 64.45. Wannan yana nuna kasashen ne suke da kashi 60 a cikin dari na jimillar hada-hadar tattalin arzikin duniya baki daya. Kasar Sin da ta zama kasa mai matukar muhimmanci a wannan hadin gwiwa, ta taimaka gaya da salo da kuma irin ci gaban da ta samu ga kasashen kungiyar.

 

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Wannan ya sa lokacin da kasar ta Sin ta yi tayin karbar bakuncin taron shugabannin APEC a shekarar 2026 wanda zai zama karo na uku ke nan da za ta karbi bakuncin taron, ba a yi wata-wata ba aka amince mata. Kasashen kungiyar suna da yakinin kasar Sin ta san hanya kuma ba ta masu mugunta a kai. Tsare-tsarenta na bude kofa ba ga kawai membobin APEC ba har ma da sauran sassan duniya, sun isa su zama shaida baro-baro a fili.

 

Wani abin birgewa da ya haifar da karsashin motsawar tattalin arzikin kasashen hadin gwaiwar APEC shi ne yadda ake ci gaba da samun raguwar haraji madaidaici a tsakanin kasashen APEC. Abin ya ragu daga kashi 17 a cikin dari a shekarar 1989 zuwa kashi 5.3 a cikin dari a shekarar 2021. Duk wannan ya samu ne saboda saboda ci gaban da ake samu na gudanar da kasuwanci mai ’yanci a tsakaninsu.

 

Da yake an riga an sahale wa kasar Sin karbar bakuncin taron shugabannin tattalin arzikin APEC a shekaru biyu masu zuwa, shin me kasar take da muradin gani ne a taron. Sashen yada labarai na ma’aikatar kula da harkokin kasashen waje na kasar Sin ya yi karin haske a kai, inda ya jaddada cewa, kasar ta shirya tsaf wajen habaka sadarwa da hadin gwiwa da sauran kasashen kungiyar game da karbar bakuncin taron na APEC a 2026 domin a hadu tare a aiwatar da Kudurin Putrajaya nan da shekarar 2040.

 

Bugu da kari, kasar tana son ganin an zurfafa gina ci gaban al’ummomin Asiya da yankin tekun Fasifik da karfafa samar da yankin ciniki mai cikakken ’yanci da samun kyakkyawan sakamako ta hanyar yin hadin gwiwa a aikace ba da fatar baki ba, kana da sanya sabon kuzari ga bunkasa tattalin arzikin Asiya da yankin Fasifik.

 

Idan muka waiwaya ga batun sada zumunci da dunkulewar duniya wuri daya bisa kyakkawar fahimta da cin moriyar juna kuma, za mu fahimci wannan hadin gwiwa na APEC yana kara nuna wa kowa da kowa cewa bai kamata nisan wuri ya zama silar kange samun hulda mai alfanu a tsakanin kasashe ba.

 

Mai karatu, ko ka san cewa tsakanin Sin da birnin Lima na kasar Peru da aka gudanar da taron shugabannin APEC karo na 31 ya kai tsawon kilomita 17,000? Amma hakan bai hana kulluwar kyakkyawar alakar Sin da yankin tekun Fasifik ba. Hakan ya kuma kara fito da aniyar kasar Sin a fili game da cewa ko a wace kurya kasa ko yanki yake a duniya matukar suna son ci gaba, kofar kasar a bude take wajen rungumar juna don a-tafi-tare-a-kuma-tsira-tare! ( Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gobara Ta Yi Sanadiyar Asarar Miliyoyin Dukiya A Kasuwar Katako Da Ke Jos

Next Post

NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

2 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

4 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

4 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

21 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

21 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

23 hours ago
Next Post
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

NAF Ta Kashe 'Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
APEC

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.