ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APEC: Nisan Wuri Ba Ya Hana Sada Zumunci Da Kulla Alheri Tsakanin Sin Da Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
LIMA, PERU - 2024/11/10: Social media Lounge view in the First day of the APEC Peru 2024 Economic Leaders Week (AELW). The Asia-Pacific Economic Cooperation (APEC), established in November 1989, is an economic forum composed of 21 Asia-Pacific economies, considered the most dynamic region in the world. (Photo by Carlos Garcia Granthon/Fotoholica Press/LightRocket via Getty Images)

LIMA, PERU - 2024/11/10: Social media Lounge view in the First day of the APEC Peru 2024 Economic Leaders Week (AELW). The Asia-Pacific Economic Cooperation (APEC), established in November 1989, is an economic forum composed of 21 Asia-Pacific economies, considered the most dynamic region in the world. (Photo by Carlos Garcia Granthon/Fotoholica Press/LightRocket via Getty Images)

Tun ana sauran mako guda a gudanar da taron shugabannin tattalin arzikin Kungiyar Hadin Gwiwar Asiya da Yankin Tekun Fasifik wato APEC, karo na 31, wanda aka kamala ranar 16 ga Nuwamban nan, kafofin watsa labarai na duniya suka yi ta yayata batun taron musamman a kasashen da abin ya shafa.

 

Hadin gwiwar da ya haifar da kafuwar kungiyar APEC a shekarar 1989 ya zama tamkar wani sabon-wata-sha-kallo saboda alfanun da yake tattare da shi da kuma zama wani madubi dai zai haska wa daukacin mutane masu rajin kawo sauyi da ci gaban al’ummar duniya na bai-daya irin turbar da ya dace kasashe musamman a matakin yankuna su bi domin fita daga kangin danniya da rashin makama wurin warware dabaibayin da ya hana ruwa gudu ga ci gaban tattalin arzikinsu.

ADVERTISEMENT
  • Buhari Ya Taya APC Murna Kan Nasararta A Jihar Ondo
  • CMG Da El Comercio Group Na Kasar Peru Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zurfafa Hadin Gwiwa

Kamar yadda alkaluma suka nuna daga majiyoyi daban-daban, daga shekarar 2014 zuwa 2022, hada-hadar tattalin arzikin kasashen kungiyar ta APEC ta habaka zuwa kimanin dala tiriliyan 64.45. Wannan yana nuna kasashen ne suke da kashi 60 a cikin dari na jimillar hada-hadar tattalin arzikin duniya baki daya. Kasar Sin da ta zama kasa mai matukar muhimmanci a wannan hadin gwiwa, ta taimaka gaya da salo da kuma irin ci gaban da ta samu ga kasashen kungiyar.

 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Wannan ya sa lokacin da kasar ta Sin ta yi tayin karbar bakuncin taron shugabannin APEC a shekarar 2026 wanda zai zama karo na uku ke nan da za ta karbi bakuncin taron, ba a yi wata-wata ba aka amince mata. Kasashen kungiyar suna da yakinin kasar Sin ta san hanya kuma ba ta masu mugunta a kai. Tsare-tsarenta na bude kofa ba ga kawai membobin APEC ba har ma da sauran sassan duniya, sun isa su zama shaida baro-baro a fili.

 

Wani abin birgewa da ya haifar da karsashin motsawar tattalin arzikin kasashen hadin gwaiwar APEC shi ne yadda ake ci gaba da samun raguwar haraji madaidaici a tsakanin kasashen APEC. Abin ya ragu daga kashi 17 a cikin dari a shekarar 1989 zuwa kashi 5.3 a cikin dari a shekarar 2021. Duk wannan ya samu ne saboda saboda ci gaban da ake samu na gudanar da kasuwanci mai ’yanci a tsakaninsu.

 

Da yake an riga an sahale wa kasar Sin karbar bakuncin taron shugabannin tattalin arzikin APEC a shekaru biyu masu zuwa, shin me kasar take da muradin gani ne a taron. Sashen yada labarai na ma’aikatar kula da harkokin kasashen waje na kasar Sin ya yi karin haske a kai, inda ya jaddada cewa, kasar ta shirya tsaf wajen habaka sadarwa da hadin gwiwa da sauran kasashen kungiyar game da karbar bakuncin taron na APEC a 2026 domin a hadu tare a aiwatar da Kudurin Putrajaya nan da shekarar 2040.

 

Bugu da kari, kasar tana son ganin an zurfafa gina ci gaban al’ummomin Asiya da yankin tekun Fasifik da karfafa samar da yankin ciniki mai cikakken ’yanci da samun kyakkyawan sakamako ta hanyar yin hadin gwiwa a aikace ba da fatar baki ba, kana da sanya sabon kuzari ga bunkasa tattalin arzikin Asiya da yankin Fasifik.

 

Idan muka waiwaya ga batun sada zumunci da dunkulewar duniya wuri daya bisa kyakkawar fahimta da cin moriyar juna kuma, za mu fahimci wannan hadin gwiwa na APEC yana kara nuna wa kowa da kowa cewa bai kamata nisan wuri ya zama silar kange samun hulda mai alfanu a tsakanin kasashe ba.

 

Mai karatu, ko ka san cewa tsakanin Sin da birnin Lima na kasar Peru da aka gudanar da taron shugabannin APEC karo na 31 ya kai tsawon kilomita 17,000? Amma hakan bai hana kulluwar kyakkyawar alakar Sin da yankin tekun Fasifik ba. Hakan ya kuma kara fito da aniyar kasar Sin a fili game da cewa ko a wace kurya kasa ko yanki yake a duniya matukar suna son ci gaba, kofar kasar a bude take wajen rungumar juna don a-tafi-tare-a-kuma-tsira-tare! ( Abdulrazaq Yahuza Jere)

APEC
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
APEC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

NAF Ta Kashe 'Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.