ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APEC: Nisan Wuri Ba Ya Hana Sada Zumunci Da Kulla Alheri Tsakanin Sin Da Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
LIMA, PERU - 2024/11/10: Social media Lounge view in the First day of the APEC Peru 2024 Economic Leaders Week (AELW). The Asia-Pacific Economic Cooperation (APEC), established in November 1989, is an economic forum composed of 21 Asia-Pacific economies, considered the most dynamic region in the world. (Photo by Carlos Garcia Granthon/Fotoholica Press/LightRocket via Getty Images)

LIMA, PERU - 2024/11/10: Social media Lounge view in the First day of the APEC Peru 2024 Economic Leaders Week (AELW). The Asia-Pacific Economic Cooperation (APEC), established in November 1989, is an economic forum composed of 21 Asia-Pacific economies, considered the most dynamic region in the world. (Photo by Carlos Garcia Granthon/Fotoholica Press/LightRocket via Getty Images)

Tun ana sauran mako guda a gudanar da taron shugabannin tattalin arzikin Kungiyar Hadin Gwiwar Asiya da Yankin Tekun Fasifik wato APEC, karo na 31, wanda aka kamala ranar 16 ga Nuwamban nan, kafofin watsa labarai na duniya suka yi ta yayata batun taron musamman a kasashen da abin ya shafa.

 

Hadin gwiwar da ya haifar da kafuwar kungiyar APEC a shekarar 1989 ya zama tamkar wani sabon-wata-sha-kallo saboda alfanun da yake tattare da shi da kuma zama wani madubi dai zai haska wa daukacin mutane masu rajin kawo sauyi da ci gaban al’ummar duniya na bai-daya irin turbar da ya dace kasashe musamman a matakin yankuna su bi domin fita daga kangin danniya da rashin makama wurin warware dabaibayin da ya hana ruwa gudu ga ci gaban tattalin arzikinsu.

ADVERTISEMENT
  • Buhari Ya Taya APC Murna Kan Nasararta A Jihar Ondo
  • CMG Da El Comercio Group Na Kasar Peru Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zurfafa Hadin Gwiwa

Kamar yadda alkaluma suka nuna daga majiyoyi daban-daban, daga shekarar 2014 zuwa 2022, hada-hadar tattalin arzikin kasashen kungiyar ta APEC ta habaka zuwa kimanin dala tiriliyan 64.45. Wannan yana nuna kasashen ne suke da kashi 60 a cikin dari na jimillar hada-hadar tattalin arzikin duniya baki daya. Kasar Sin da ta zama kasa mai matukar muhimmanci a wannan hadin gwiwa, ta taimaka gaya da salo da kuma irin ci gaban da ta samu ga kasashen kungiyar.

 

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Wannan ya sa lokacin da kasar ta Sin ta yi tayin karbar bakuncin taron shugabannin APEC a shekarar 2026 wanda zai zama karo na uku ke nan da za ta karbi bakuncin taron, ba a yi wata-wata ba aka amince mata. Kasashen kungiyar suna da yakinin kasar Sin ta san hanya kuma ba ta masu mugunta a kai. Tsare-tsarenta na bude kofa ba ga kawai membobin APEC ba har ma da sauran sassan duniya, sun isa su zama shaida baro-baro a fili.

 

Wani abin birgewa da ya haifar da karsashin motsawar tattalin arzikin kasashen hadin gwaiwar APEC shi ne yadda ake ci gaba da samun raguwar haraji madaidaici a tsakanin kasashen APEC. Abin ya ragu daga kashi 17 a cikin dari a shekarar 1989 zuwa kashi 5.3 a cikin dari a shekarar 2021. Duk wannan ya samu ne saboda saboda ci gaban da ake samu na gudanar da kasuwanci mai ’yanci a tsakaninsu.

 

Da yake an riga an sahale wa kasar Sin karbar bakuncin taron shugabannin tattalin arzikin APEC a shekaru biyu masu zuwa, shin me kasar take da muradin gani ne a taron. Sashen yada labarai na ma’aikatar kula da harkokin kasashen waje na kasar Sin ya yi karin haske a kai, inda ya jaddada cewa, kasar ta shirya tsaf wajen habaka sadarwa da hadin gwiwa da sauran kasashen kungiyar game da karbar bakuncin taron na APEC a 2026 domin a hadu tare a aiwatar da Kudurin Putrajaya nan da shekarar 2040.

 

Bugu da kari, kasar tana son ganin an zurfafa gina ci gaban al’ummomin Asiya da yankin tekun Fasifik da karfafa samar da yankin ciniki mai cikakken ’yanci da samun kyakkyawan sakamako ta hanyar yin hadin gwiwa a aikace ba da fatar baki ba, kana da sanya sabon kuzari ga bunkasa tattalin arzikin Asiya da yankin Fasifik.

 

Idan muka waiwaya ga batun sada zumunci da dunkulewar duniya wuri daya bisa kyakkawar fahimta da cin moriyar juna kuma, za mu fahimci wannan hadin gwiwa na APEC yana kara nuna wa kowa da kowa cewa bai kamata nisan wuri ya zama silar kange samun hulda mai alfanu a tsakanin kasashe ba.

 

Mai karatu, ko ka san cewa tsakanin Sin da birnin Lima na kasar Peru da aka gudanar da taron shugabannin APEC karo na 31 ya kai tsawon kilomita 17,000? Amma hakan bai hana kulluwar kyakkyawar alakar Sin da yankin tekun Fasifik ba. Hakan ya kuma kara fito da aniyar kasar Sin a fili game da cewa ko a wace kurya kasa ko yanki yake a duniya matukar suna son ci gaba, kofar kasar a bude take wajen rungumar juna don a-tafi-tare-a-kuma-tsira-tare! ( Abdulrazaq Yahuza Jere)

APEC
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
APEC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

NAF Ta Kashe 'Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.