ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APEC: Nisan Wuri Ba Ya Hana Sada Zumunci Da Kulla Alheri Tsakanin Sin Da Kasashen Duniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
LIMA, PERU - 2024/11/10: Social media Lounge view in the First day of the APEC Peru 2024 Economic Leaders Week (AELW). The Asia-Pacific Economic Cooperation (APEC), established in November 1989, is an economic forum composed of 21 Asia-Pacific economies, considered the most dynamic region in the world. (Photo by Carlos Garcia Granthon/Fotoholica Press/LightRocket via Getty Images)

LIMA, PERU - 2024/11/10: Social media Lounge view in the First day of the APEC Peru 2024 Economic Leaders Week (AELW). The Asia-Pacific Economic Cooperation (APEC), established in November 1989, is an economic forum composed of 21 Asia-Pacific economies, considered the most dynamic region in the world. (Photo by Carlos Garcia Granthon/Fotoholica Press/LightRocket via Getty Images)

Tun ana sauran mako guda a gudanar da taron shugabannin tattalin arzikin Kungiyar Hadin Gwiwar Asiya da Yankin Tekun Fasifik wato APEC, karo na 31, wanda aka kamala ranar 16 ga Nuwamban nan, kafofin watsa labarai na duniya suka yi ta yayata batun taron musamman a kasashen da abin ya shafa.

 

Hadin gwiwar da ya haifar da kafuwar kungiyar APEC a shekarar 1989 ya zama tamkar wani sabon-wata-sha-kallo saboda alfanun da yake tattare da shi da kuma zama wani madubi dai zai haska wa daukacin mutane masu rajin kawo sauyi da ci gaban al’ummar duniya na bai-daya irin turbar da ya dace kasashe musamman a matakin yankuna su bi domin fita daga kangin danniya da rashin makama wurin warware dabaibayin da ya hana ruwa gudu ga ci gaban tattalin arzikinsu.

ADVERTISEMENT
  • Buhari Ya Taya APC Murna Kan Nasararta A Jihar Ondo
  • CMG Da El Comercio Group Na Kasar Peru Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zurfafa Hadin Gwiwa

Kamar yadda alkaluma suka nuna daga majiyoyi daban-daban, daga shekarar 2014 zuwa 2022, hada-hadar tattalin arzikin kasashen kungiyar ta APEC ta habaka zuwa kimanin dala tiriliyan 64.45. Wannan yana nuna kasashen ne suke da kashi 60 a cikin dari na jimillar hada-hadar tattalin arzikin duniya baki daya. Kasar Sin da ta zama kasa mai matukar muhimmanci a wannan hadin gwiwa, ta taimaka gaya da salo da kuma irin ci gaban da ta samu ga kasashen kungiyar.

 

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Wannan ya sa lokacin da kasar ta Sin ta yi tayin karbar bakuncin taron shugabannin APEC a shekarar 2026 wanda zai zama karo na uku ke nan da za ta karbi bakuncin taron, ba a yi wata-wata ba aka amince mata. Kasashen kungiyar suna da yakinin kasar Sin ta san hanya kuma ba ta masu mugunta a kai. Tsare-tsarenta na bude kofa ba ga kawai membobin APEC ba har ma da sauran sassan duniya, sun isa su zama shaida baro-baro a fili.

 

Wani abin birgewa da ya haifar da karsashin motsawar tattalin arzikin kasashen hadin gwaiwar APEC shi ne yadda ake ci gaba da samun raguwar haraji madaidaici a tsakanin kasashen APEC. Abin ya ragu daga kashi 17 a cikin dari a shekarar 1989 zuwa kashi 5.3 a cikin dari a shekarar 2021. Duk wannan ya samu ne saboda saboda ci gaban da ake samu na gudanar da kasuwanci mai ’yanci a tsakaninsu.

 

Da yake an riga an sahale wa kasar Sin karbar bakuncin taron shugabannin tattalin arzikin APEC a shekaru biyu masu zuwa, shin me kasar take da muradin gani ne a taron. Sashen yada labarai na ma’aikatar kula da harkokin kasashen waje na kasar Sin ya yi karin haske a kai, inda ya jaddada cewa, kasar ta shirya tsaf wajen habaka sadarwa da hadin gwiwa da sauran kasashen kungiyar game da karbar bakuncin taron na APEC a 2026 domin a hadu tare a aiwatar da Kudurin Putrajaya nan da shekarar 2040.

 

Bugu da kari, kasar tana son ganin an zurfafa gina ci gaban al’ummomin Asiya da yankin tekun Fasifik da karfafa samar da yankin ciniki mai cikakken ’yanci da samun kyakkyawan sakamako ta hanyar yin hadin gwiwa a aikace ba da fatar baki ba, kana da sanya sabon kuzari ga bunkasa tattalin arzikin Asiya da yankin Fasifik.

 

Idan muka waiwaya ga batun sada zumunci da dunkulewar duniya wuri daya bisa kyakkawar fahimta da cin moriyar juna kuma, za mu fahimci wannan hadin gwiwa na APEC yana kara nuna wa kowa da kowa cewa bai kamata nisan wuri ya zama silar kange samun hulda mai alfanu a tsakanin kasashe ba.

 

Mai karatu, ko ka san cewa tsakanin Sin da birnin Lima na kasar Peru da aka gudanar da taron shugabannin APEC karo na 31 ya kai tsawon kilomita 17,000? Amma hakan bai hana kulluwar kyakkyawar alakar Sin da yankin tekun Fasifik ba. Hakan ya kuma kara fito da aniyar kasar Sin a fili game da cewa ko a wace kurya kasa ko yanki yake a duniya matukar suna son ci gaba, kofar kasar a bude take wajen rungumar juna don a-tafi-tare-a-kuma-tsira-tare! ( Abdulrazaq Yahuza Jere)

APEC
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
APEC
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

NAF Ta Kashe 'Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.