Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta kammala Sayan dan wasan tsakiya na kungiyar FC Porto, Fabio Vieira, akan kudi fam miliyan 34.
Tun a satin daya gabata ne dai kungiyoyin biyu suka cimma matsaya bayan doguwar tattauna wa a tsakanin su.
Vieira yana daya daga cikin ‘yan wasan da kociyan kungiyar, Mikel Arteta ya bukaci kungiyar ta siyo masa domin bunkasa tawagar a kakar wasa mai zuwa.
Bayan kammala Sayan Vieira, yanzu hankalin Arsenal zai karkata ga neman dan wasan Manchester City, Gabriel Jesus, wanda ake saran nan gaba kadan za’a shiga tattauna wa tsakanin kungiyoyin biyu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp