• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asalin Abin Da Ya Sa Wata Mata Kashe Mijinta A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Asalin Abin Da Ya Sa Wata Mata Kashe Mijinta A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan za ku iya tunawa dai a ranar 5 ga watan Yuli ne wata mata mai suna Maimunatu Sulaiman da ke zama a unguwar Kofar Dumi cikin kwaryar Bauchi ta kashe mijinta Aliyu Mohammad sakamakon rashin jituwar da ta shiga tsakaninsu.

Bayanai da ke fitowa daga bakunan mutanen yankin unguwar na cewa an samu rashin jituwar a tsakanin miji da matar ne sakamakon yunkurin da Aliyu mijin ya yi na kara aure.

  • Daminar Bana: Sarkin Bauchi Ya Jagoranci Addu’ar Rokon Ruwa

Kazalika, an labarto cewar matar ta daddaba wa mijin nata wuka ne a kirjinsa da hakan ya janyo sanadin mutuwarsa.

Lamarin dai ya faru ne a ranar 5 ga watan Yulin 2023 a gidan ma’auratan da ke wannan adireshin na unguwar Kofar Dumi.
Domin jin yadda ainihin lamarin ya kasance, LEADERSHIP Hausa ta zanta da daya daga cikin ‘yar uwar mamacin inda ta fayyace zare da abawa.

Ta shaida cewar, akwai maganar mijin zai kara aure amma ya bijiro da maganar ne kawai domin rashin jin dadin zama da matar tasa.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Sannan, ta ce, matar Maimunatu ta na da wasu kawaye da suka janyo mata lalacewar dabi’arta duk da cewa sun yi aure na soyayya da mijinta.

“Shi dai dan uwanmu ne, amma da yake kuma gidanmu na kusa da su, kusan kullum yana shigowa gidanmu sau tarin lokaci ya kan yi korafi a kanta kan wasu dabi’unta da bai gamsu da su ba, hakan kuma yana yawan janyo musu yin fada a tsakani.

“Sannan ita din tana shaye-shaye, domin a ranar da aka yi kisan ma an duba dakinta an ga nau’ikan kayan maye wasu ma har wari suke yi,” a cewar ‘yar uwar mamacin da ta nemi a sakaya sunanta saboda wasu dalilai.
Ta ci gaba da bayani cewa, “Abin da aka iya ganowa shi ne, ta sanya masa maganin sanya barci ne a zobo ta yadda koda za ta caka masa wukar ma ba zai iya komai ba; yadda ta caccaka masa wukar a wajen ko motsawa bai yi ba.

“Lokacin da wansa ya shiga dakin sai ya kira babansa cikin firgici ya ce Baffa ka zo an kashe Ali domin ya ga abin da ke faruwa.
Sai shi baban nasa ya zare wukar daga jikinsa.

‘Lokacin da ta cakka masa wukar, ita ma ta dan yanka kanta, kawuna ne ma ya yi mata dinki.

Da farko kowa ya dauka barayi ne suka shigo suka kashe shi suka kuma jikkata ita matar, dama haka ta so yi domin bayan da ta kashe shi ta yanki kanta sai ta kwanta a kan gawarsa domin jini ya bata mata jiki sai ta yi kamar ta suma.

“Hakan ya sanya jama’a suka dauka ita ma barayi ne suka jikkata su duka. Sai aka dauke ta zuwa asibiti.
“Daga baya da aka gane ba barayi ba ne sai labarin ya canza kuma. Daman ta taba masa irin haka.

Ana saura kwana biyu ma ta kashe shi ta dauki dankwali ta shake masa wuya har wuyan ya kumbura.

“Da ya je gidan Dadarsa sai take tambayarsa meke faruwa sai ya gaya Mata abubuwan da suke faruwa sannan ye ce maza shi kam zai rabu da ita saboda ta na yunkurin kasheshi.”

‘Yar uwan ta shi ta bayyana cewar marigayi Aliyu na sana’ar sanya tayels ne. Ta kara da cewa, akwai zargin da ake yi wa matar tasa na cewa tana mu’amala da wasu muggan kawaye da abokai da suke hure mata kunne, “Ta na da wasu kawaye da take kawowa su barnata gidan.

Sannan in ta je makaranta ba ta dawowa da wuri hakan ya fara sanya zargi a tsakaninsu.
“Tana da aurensa amma ta na da wasu samarin a waje. Abin da zai baka mamaki auren soyayya suka yi amma daga baya ta samu wasu kawaye da abokai gurbatattu suka daurata a mummunar hanya.

“Tana sonsa sosai shi ma yana sonta da farko, amma daga baya da ta samu masu hure mata kunne shi kenan ta baci. Akwai wani da ya mata alkawarin zai aure ta muddin ta rabu da mijinta mai rasuwa.
“Babanta Birkila ne a Gombe ya ke, da yake ya ga kyawun dabi’un marigayin sai ya hada sa aure da ‘yarsa a she ita ce ajalinsa.
“Ya sha kokarin rabuwa da ita amma sai ya ce in ya sake ta bai da kudin da zai kara aure.”

Ta kuma tabbatar da shi marigayin da kansa ya fada kafin ta kashe shi cewar matar tasa tana dauke da juna biyu na wata biyu amma ta zubar da cikin.

Ta misalta marigayin a matsayin mutum na kwarai wanda bai shiga sabgogin kowa sai hakan ya zama dole balle har ya yi fada.
Sai dai a bangaren rundunar ‘yansandan Jihar Bauchi kuwa, sun ce kawo yanzu sun cafke ita Maimunatu bisa zargin kisan kai.
A sanarwar da mai rikon kakakin ‘yansanda Jihar Bauchi, ASP Aminu Gimba Ahmed ya fitar a ranar Juma’a na cewa, “A ranar 5 ga watan Yulin 2023 jami’an caji ofis din ‘yansanda da ke Township, Bauchi sun kama wata Maimunatu Sulaiman bisa zarginta da aikata kisan kai.

“Lokacin da jami’an suka samu rahoton faruwar lamarin, sun garzaya zuwa inda lamarin ya faru tare da daukar wanda tsautsayin ya rutsa da shi da ita kanta wacce ake zargi zuwa asibitin koyarwa na Abubakar Tafawa Balewa Teaching Hospital (ATBUTH), Bauchi domin kokarin nema musu kulawar Likitoci.”

“Amma Likitoci sun tabbatar mutuwar mijin sakamakon raunuka da ya samu a kirjinsa, yayin da ita kuma wacce ake zargin ta samu wasu ‘yan raunuka kadan a cikinta.”
Binciken ‘yansanda na farko-farko na nuni da cewa wacce ake zargin Maimuna Suleiman ta soki mijinta Aliyu ne a kirjinsa sakamakon rashin jituwar da ta barke a tsakaninsu a gidansu na aure.

A lokacin binciken wacce ake zargin ta amsa laifinta da kanta a cewar sanarwar ta ‘yansanda.

Kan hakan, kwamishinan ‘yansandan Jihar Bauchi CP Auwal Musa Mohammad, ya umarci a tura lamarin zuwa sashen kula da manyan laifuka (SCID) domin zurfafa binciken da gano musabbabin faruwar lamarin.

Ya ce za a gurfanar da wacce ake zargin da za a aka kammala gudanar da binciken ‘yansanda.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kan Mage Ya Waye, Turawan Yamma A Sake Lale Kan Yamadidin “Tarkon Bashin Sin”

Next Post

Gini Ya Yi Ajalin Yara 2 Legas

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

18 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

19 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

21 hours ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

1 week ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

1 week ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

1 week ago
Next Post
Gini Ya Yi Ajalin Yara 2 Legas

Gini Ya Yi Ajalin Yara 2 Legas

LABARAI MASU NASABA

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.