ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
Sojoji

An kama sojoji biyu bisa alaka da rushewar wani kamfanin hada magungunan bogi a Kasuwar Alaba International, Ojo, Jihar Legas.

A baya, PUNCH Metro ta ruwaito cewa Kwamishinan ‘Yansanda, Olohundare Jimoh, ya sanar da gano tare da rufe wurin sarrafa magungunan a yankin Ojo na jihar.

  • An Bukaci Amurka Da Ta Kauracewa Sanya Wasu Sassa Na Muzgunawa Kasar Sin Cikin Kudurin Dokar Tsaron Kasa
  • Yawan Jarin Waje Da Kasar Sin Ta Yi Amfani Da Shi A Watan Nuwamban Bana Ya Karu Da Kaso 26.1%

Da yake magana da ‘yan jarida a ranar Laraba a ginin da aka kai samame a titin Alhaji Oki, Mosafejo, Ojo, shugaban ‘yansandan ya bayyana aikin a matsayin babban ci gaba wajen kare lafiyar jama’a.

ADVERTISEMENT

Harantaccen wurin ana hada magungunan bogi da aka shirya domin sayarwa da kuma amfani da su ga jama’a.

Wata majiya daga rundunar ‘yansanda, wadda ta nemi a sakaya sunanta saboda ba ta da izinin magana kan lamarin, ta shaida wa wakilinmu a ranar Lahadi cewa ana amfani da sojojin wajen rarraba magungunan bogin zuwa sassa daban-daban na Jihar Legas.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Majiyar ta kara da cewa wani tawagar ‘yan sanda daga Ofishin ‘Yansanda na Ojo, karkashin jagorancin Dibisional Police Officer, CSP Olaifa Omolola, ta tare motar yayin da take dauke da magungunan tana kan hanyarta zuwa inda za a kai su.

“Wata tawagar ‘yansanda daga Ofishin ‘Yansanda na Ojo, karkashin jagorancin DPO, CSP Olaifa Omolola, sun tare wata mota dauke da magunguna a cikin motar haya a wani lokaci a watan Satumban 2025, kusa da tashar mota ta St Patrick a Kasuwar Alaba International.

“Daga bisani DPO ta tura jami’an bincike zuwa yankin, inda aka kama wasu mutane biyu sanye da kayan sojoji tare da magungunan da wa’adin amfaninsu suka kare,” in ji majiyar.

A cewar majiyar ‘yansandan, aikin ya kasance mai matukar wahala, domin da farko sojojin sun ki bayyana inda magungunan suka fito da kuma inda ake shirin kai su.

“DPO da kanta ce ta jagoranci binciken. Ta hanyar jajircewarta ne aka gano inda ake hada magungunan.

“Yayin binciken, an gano cewa mutumin da ya fara wannan kasuwanci tun asali ya mutu, amma matarsa da ma’aikatansa sun ci gaba da wannan haramtacciyar harkar,” in ji majiyar.

Haka kuma an gano cewa CSP Olaifa ta ki amincewa da tayin cin hanci mai yawa daga wasu mutane da ba a san ko su waye ba, wadanda ake zargin su ne ke da hannu a harkar magungunan bogi, inda suke yawan kiran ta a waya.

“DPO ta fara samun kiran waya masu ban mamaki daga wurare daban-daban, inda ake tayin belin wadanda ake zargi tare da rokon ta ta fadi duk farashin da take so domin a rufe lamarin, amma ta yi watsi da tayin tare da yin abin da ya dace ta hanyar mika shari’ar inda ya dace,” in ji majiyar.

An kuma gano cewa mutane biyar ne ke da hannu wajen hada magungunan bogi da kuma canza ranakun karewar wa’adin amfani da su, kuma sun fi gudanar da ayyukansu ne cikin dare.

Magungunan bogin da aka kwato daga hannun kungiyar sun hada da ampicillin, promethazine hydrochloride, kuinine hydrochloride, da kuma nau’o’in magungunan zazzabin cizon sauro da sirinji daban-daban.

Wakilinmu ya kuma gano cewa ‘yansanda sun bi diddigin wasu daga cikin magungunan da wa’adinsu ya kare zuwa manyan shagunan magunguna a Festac Town, Satellite Town da kuma Lagos Island.

Ba a samu jin ta bakin kakakin rundunar ‘yansandan jihar Abimbola Adebisi, ba saboda ba ta amsa kiran wayoyinta ba.

Sakon kar-ta-kwana (SMS) da aka aike mata ma ba ta amsa ba har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto.”

Sojoji
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
RIGATA 2026: Al’umma Daga Ciki Da Wajen Nijeriya Za Su Baje Kolin Al’adun Gargajiya

RIGATA 2026: Al'umma Daga Ciki Da Wajen Nijeriya Za Su Baje Kolin Al’adun Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.