ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Sojoji

An kama sojoji biyu bisa alaka da rushewar wani kamfanin hada magungunan bogi a Kasuwar Alaba International, Ojo, Jihar Legas.

A baya, PUNCH Metro ta ruwaito cewa Kwamishinan ‘Yansanda, Olohundare Jimoh, ya sanar da gano tare da rufe wurin sarrafa magungunan a yankin Ojo na jihar.

  • An Bukaci Amurka Da Ta Kauracewa Sanya Wasu Sassa Na Muzgunawa Kasar Sin Cikin Kudurin Dokar Tsaron Kasa
  • Yawan Jarin Waje Da Kasar Sin Ta Yi Amfani Da Shi A Watan Nuwamban Bana Ya Karu Da Kaso 26.1%

Da yake magana da ‘yan jarida a ranar Laraba a ginin da aka kai samame a titin Alhaji Oki, Mosafejo, Ojo, shugaban ‘yansandan ya bayyana aikin a matsayin babban ci gaba wajen kare lafiyar jama’a.

ADVERTISEMENT

Harantaccen wurin ana hada magungunan bogi da aka shirya domin sayarwa da kuma amfani da su ga jama’a.

Wata majiya daga rundunar ‘yansanda, wadda ta nemi a sakaya sunanta saboda ba ta da izinin magana kan lamarin, ta shaida wa wakilinmu a ranar Lahadi cewa ana amfani da sojojin wajen rarraba magungunan bogin zuwa sassa daban-daban na Jihar Legas.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Majiyar ta kara da cewa wani tawagar ‘yan sanda daga Ofishin ‘Yansanda na Ojo, karkashin jagorancin Dibisional Police Officer, CSP Olaifa Omolola, ta tare motar yayin da take dauke da magungunan tana kan hanyarta zuwa inda za a kai su.

“Wata tawagar ‘yansanda daga Ofishin ‘Yansanda na Ojo, karkashin jagorancin DPO, CSP Olaifa Omolola, sun tare wata mota dauke da magunguna a cikin motar haya a wani lokaci a watan Satumban 2025, kusa da tashar mota ta St Patrick a Kasuwar Alaba International.

“Daga bisani DPO ta tura jami’an bincike zuwa yankin, inda aka kama wasu mutane biyu sanye da kayan sojoji tare da magungunan da wa’adin amfaninsu suka kare,” in ji majiyar.

A cewar majiyar ‘yansandan, aikin ya kasance mai matukar wahala, domin da farko sojojin sun ki bayyana inda magungunan suka fito da kuma inda ake shirin kai su.

“DPO da kanta ce ta jagoranci binciken. Ta hanyar jajircewarta ne aka gano inda ake hada magungunan.

“Yayin binciken, an gano cewa mutumin da ya fara wannan kasuwanci tun asali ya mutu, amma matarsa da ma’aikatansa sun ci gaba da wannan haramtacciyar harkar,” in ji majiyar.

Haka kuma an gano cewa CSP Olaifa ta ki amincewa da tayin cin hanci mai yawa daga wasu mutane da ba a san ko su waye ba, wadanda ake zargin su ne ke da hannu a harkar magungunan bogi, inda suke yawan kiran ta a waya.

“DPO ta fara samun kiran waya masu ban mamaki daga wurare daban-daban, inda ake tayin belin wadanda ake zargi tare da rokon ta ta fadi duk farashin da take so domin a rufe lamarin, amma ta yi watsi da tayin tare da yin abin da ya dace ta hanyar mika shari’ar inda ya dace,” in ji majiyar.

An kuma gano cewa mutane biyar ne ke da hannu wajen hada magungunan bogi da kuma canza ranakun karewar wa’adin amfani da su, kuma sun fi gudanar da ayyukansu ne cikin dare.

Magungunan bogin da aka kwato daga hannun kungiyar sun hada da ampicillin, promethazine hydrochloride, kuinine hydrochloride, da kuma nau’o’in magungunan zazzabin cizon sauro da sirinji daban-daban.

Wakilinmu ya kuma gano cewa ‘yansanda sun bi diddigin wasu daga cikin magungunan da wa’adinsu ya kare zuwa manyan shagunan magunguna a Festac Town, Satellite Town da kuma Lagos Island.

Ba a samu jin ta bakin kakakin rundunar ‘yansandan jihar Abimbola Adebisi, ba saboda ba ta amsa kiran wayoyinta ba.

Sakon kar-ta-kwana (SMS) da aka aike mata ma ba ta amsa ba har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto.”

Sojoji
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
RIGATA 2026: Al’umma Daga Ciki Da Wajen Nijeriya Za Su Baje Kolin Al’adun Gargajiya

RIGATA 2026: Al'umma Daga Ciki Da Wajen Nijeriya Za Su Baje Kolin Al’adun Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.