ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
Sojoji

An kama sojoji biyu bisa alaka da rushewar wani kamfanin hada magungunan bogi a Kasuwar Alaba International, Ojo, Jihar Legas.

A baya, PUNCH Metro ta ruwaito cewa Kwamishinan ‘Yansanda, Olohundare Jimoh, ya sanar da gano tare da rufe wurin sarrafa magungunan a yankin Ojo na jihar.

  • An Bukaci Amurka Da Ta Kauracewa Sanya Wasu Sassa Na Muzgunawa Kasar Sin Cikin Kudurin Dokar Tsaron Kasa
  • Yawan Jarin Waje Da Kasar Sin Ta Yi Amfani Da Shi A Watan Nuwamban Bana Ya Karu Da Kaso 26.1%

Da yake magana da ‘yan jarida a ranar Laraba a ginin da aka kai samame a titin Alhaji Oki, Mosafejo, Ojo, shugaban ‘yansandan ya bayyana aikin a matsayin babban ci gaba wajen kare lafiyar jama’a.

ADVERTISEMENT

Harantaccen wurin ana hada magungunan bogi da aka shirya domin sayarwa da kuma amfani da su ga jama’a.

Wata majiya daga rundunar ‘yansanda, wadda ta nemi a sakaya sunanta saboda ba ta da izinin magana kan lamarin, ta shaida wa wakilinmu a ranar Lahadi cewa ana amfani da sojojin wajen rarraba magungunan bogin zuwa sassa daban-daban na Jihar Legas.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Majiyar ta kara da cewa wani tawagar ‘yan sanda daga Ofishin ‘Yansanda na Ojo, karkashin jagorancin Dibisional Police Officer, CSP Olaifa Omolola, ta tare motar yayin da take dauke da magungunan tana kan hanyarta zuwa inda za a kai su.

“Wata tawagar ‘yansanda daga Ofishin ‘Yansanda na Ojo, karkashin jagorancin DPO, CSP Olaifa Omolola, sun tare wata mota dauke da magunguna a cikin motar haya a wani lokaci a watan Satumban 2025, kusa da tashar mota ta St Patrick a Kasuwar Alaba International.

“Daga bisani DPO ta tura jami’an bincike zuwa yankin, inda aka kama wasu mutane biyu sanye da kayan sojoji tare da magungunan da wa’adin amfaninsu suka kare,” in ji majiyar.

A cewar majiyar ‘yansandan, aikin ya kasance mai matukar wahala, domin da farko sojojin sun ki bayyana inda magungunan suka fito da kuma inda ake shirin kai su.

“DPO da kanta ce ta jagoranci binciken. Ta hanyar jajircewarta ne aka gano inda ake hada magungunan.

“Yayin binciken, an gano cewa mutumin da ya fara wannan kasuwanci tun asali ya mutu, amma matarsa da ma’aikatansa sun ci gaba da wannan haramtacciyar harkar,” in ji majiyar.

Haka kuma an gano cewa CSP Olaifa ta ki amincewa da tayin cin hanci mai yawa daga wasu mutane da ba a san ko su waye ba, wadanda ake zargin su ne ke da hannu a harkar magungunan bogi, inda suke yawan kiran ta a waya.

“DPO ta fara samun kiran waya masu ban mamaki daga wurare daban-daban, inda ake tayin belin wadanda ake zargi tare da rokon ta ta fadi duk farashin da take so domin a rufe lamarin, amma ta yi watsi da tayin tare da yin abin da ya dace ta hanyar mika shari’ar inda ya dace,” in ji majiyar.

An kuma gano cewa mutane biyar ne ke da hannu wajen hada magungunan bogi da kuma canza ranakun karewar wa’adin amfani da su, kuma sun fi gudanar da ayyukansu ne cikin dare.

Magungunan bogin da aka kwato daga hannun kungiyar sun hada da ampicillin, promethazine hydrochloride, kuinine hydrochloride, da kuma nau’o’in magungunan zazzabin cizon sauro da sirinji daban-daban.

Wakilinmu ya kuma gano cewa ‘yansanda sun bi diddigin wasu daga cikin magungunan da wa’adinsu ya kare zuwa manyan shagunan magunguna a Festac Town, Satellite Town da kuma Lagos Island.

Ba a samu jin ta bakin kakakin rundunar ‘yansandan jihar Abimbola Adebisi, ba saboda ba ta amsa kiran wayoyinta ba.

Sakon kar-ta-kwana (SMS) da aka aike mata ma ba ta amsa ba har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto.”

Sojoji
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
RIGATA 2026: Al’umma Daga Ciki Da Wajen Nijeriya Za Su Baje Kolin Al’adun Gargajiya

RIGATA 2026: Al'umma Daga Ciki Da Wajen Nijeriya Za Su Baje Kolin Al’adun Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.