ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Sojoji Biyu A Legas Kan Alaka Da Sarrafa Magungunan Jabu

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
Sojoji

An kama sojoji biyu bisa alaka da rushewar wani kamfanin hada magungunan bogi a Kasuwar Alaba International, Ojo, Jihar Legas.

A baya, PUNCH Metro ta ruwaito cewa Kwamishinan ‘Yansanda, Olohundare Jimoh, ya sanar da gano tare da rufe wurin sarrafa magungunan a yankin Ojo na jihar.

  • An Bukaci Amurka Da Ta Kauracewa Sanya Wasu Sassa Na Muzgunawa Kasar Sin Cikin Kudurin Dokar Tsaron Kasa
  • Yawan Jarin Waje Da Kasar Sin Ta Yi Amfani Da Shi A Watan Nuwamban Bana Ya Karu Da Kaso 26.1%

Da yake magana da ‘yan jarida a ranar Laraba a ginin da aka kai samame a titin Alhaji Oki, Mosafejo, Ojo, shugaban ‘yansandan ya bayyana aikin a matsayin babban ci gaba wajen kare lafiyar jama’a.

ADVERTISEMENT

Harantaccen wurin ana hada magungunan bogi da aka shirya domin sayarwa da kuma amfani da su ga jama’a.

Wata majiya daga rundunar ‘yansanda, wadda ta nemi a sakaya sunanta saboda ba ta da izinin magana kan lamarin, ta shaida wa wakilinmu a ranar Lahadi cewa ana amfani da sojojin wajen rarraba magungunan bogin zuwa sassa daban-daban na Jihar Legas.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Majiyar ta kara da cewa wani tawagar ‘yan sanda daga Ofishin ‘Yansanda na Ojo, karkashin jagorancin Dibisional Police Officer, CSP Olaifa Omolola, ta tare motar yayin da take dauke da magungunan tana kan hanyarta zuwa inda za a kai su.

“Wata tawagar ‘yansanda daga Ofishin ‘Yansanda na Ojo, karkashin jagorancin DPO, CSP Olaifa Omolola, sun tare wata mota dauke da magunguna a cikin motar haya a wani lokaci a watan Satumban 2025, kusa da tashar mota ta St Patrick a Kasuwar Alaba International.

“Daga bisani DPO ta tura jami’an bincike zuwa yankin, inda aka kama wasu mutane biyu sanye da kayan sojoji tare da magungunan da wa’adin amfaninsu suka kare,” in ji majiyar.

A cewar majiyar ‘yansandan, aikin ya kasance mai matukar wahala, domin da farko sojojin sun ki bayyana inda magungunan suka fito da kuma inda ake shirin kai su.

“DPO da kanta ce ta jagoranci binciken. Ta hanyar jajircewarta ne aka gano inda ake hada magungunan.

“Yayin binciken, an gano cewa mutumin da ya fara wannan kasuwanci tun asali ya mutu, amma matarsa da ma’aikatansa sun ci gaba da wannan haramtacciyar harkar,” in ji majiyar.

Haka kuma an gano cewa CSP Olaifa ta ki amincewa da tayin cin hanci mai yawa daga wasu mutane da ba a san ko su waye ba, wadanda ake zargin su ne ke da hannu a harkar magungunan bogi, inda suke yawan kiran ta a waya.

“DPO ta fara samun kiran waya masu ban mamaki daga wurare daban-daban, inda ake tayin belin wadanda ake zargi tare da rokon ta ta fadi duk farashin da take so domin a rufe lamarin, amma ta yi watsi da tayin tare da yin abin da ya dace ta hanyar mika shari’ar inda ya dace,” in ji majiyar.

An kuma gano cewa mutane biyar ne ke da hannu wajen hada magungunan bogi da kuma canza ranakun karewar wa’adin amfani da su, kuma sun fi gudanar da ayyukansu ne cikin dare.

Magungunan bogin da aka kwato daga hannun kungiyar sun hada da ampicillin, promethazine hydrochloride, kuinine hydrochloride, da kuma nau’o’in magungunan zazzabin cizon sauro da sirinji daban-daban.

Wakilinmu ya kuma gano cewa ‘yansanda sun bi diddigin wasu daga cikin magungunan da wa’adinsu ya kare zuwa manyan shagunan magunguna a Festac Town, Satellite Town da kuma Lagos Island.

Ba a samu jin ta bakin kakakin rundunar ‘yansandan jihar Abimbola Adebisi, ba saboda ba ta amsa kiran wayoyinta ba.

Sakon kar-ta-kwana (SMS) da aka aike mata ma ba ta amsa ba har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto.”

Sojoji
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
RIGATA 2026: Al’umma Daga Ciki Da Wajen Nijeriya Za Su Baje Kolin Al’adun Gargajiya

RIGATA 2026: Al'umma Daga Ciki Da Wajen Nijeriya Za Su Baje Kolin Al’adun Gargajiya

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.