• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun Bunkasa Aikin Noma na Kasa (NADF), da Hukumar SRRBDA da kuma OCP ta Afirka, sun yi hadaka tare da kaddamar da hektar noma 50, domin yin noma na tsawon shekara daya a Dam din Sabke da ke Jihar Katsina.

Amfanin gona kala hudu ake sa ran nomawa a cikin wannan kakada, wadanda suka hada da; Masara, Dawa, Waken Soya da kuma Farin Wake.

  • ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?
  • Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

A cikin sanarwar da Asusun ya fitar ya bayyana cewa, za a noma wadannan amfanin ne a fannin noma, domin samun riba.

Babban Sakaren Asusun, Mohammed Ibrahim ya bayyana hakan ne a jawabinsa a wajen rattaba hannun yarjejeniyar gudanar da aikin.

Ya bayyana cewa, za a gudanar da aikin, biyo bayan sakamakon dabarun hadakar da aka kulla; domin fara yin aikin noman, wanda za a yi har zuwa zagayowar wani watan na damina.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Ya sanar da cewa, manufar aikin ta faro ne, biyo bayan wata ziyarar aiki da Asusun ya ka Jihar Katsina.

“Asusun na NADF, ya dauki kwararan matakai; musamman ta hanyar zuba kudade don yin amfani da Dam din na Sabke da ke Jihar Katsina, domin yin amfani da ruwan da ke cikin Dam, don yin noma na zamani“, in ji Mohammed.

“OCP na Afirka, na da kwararru wadanda tuni suka auna yanayin kadadar da a gudanar da aikin, musamman duba da cewa; za a iya yin amfani da ruwan Dam din na  Sabke, wajen gudanar da aikin”, a cewarsa.

Ya kara da cewa, Bankin shi kuma zai samar da wadatattun kudaden da za a yi aikin, wanda kuma Asusun na NADF zai kasance mai sanya ido kan aikin.

Ya kuma bayyana gamsuwar cewa, aikin zai kasance na zamani.

Shi kuwa a nasa jawabin, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda ya sanar da cewa; gwamnatinsa za ta bai wa aikin goyon bayan da ya dace.

“A lokacin da aka gabatar min da batun wannan aiki, nan da nan na aminta da shi, duba da irin dimbin alfanun da ke tattare da aikin, musamman wajen kara bunkasa tattalin arzikin Jihar Katsina da kuma rayuwar ‘yan jihar baki-daya“, in Radda.

“Burinmu shi ne, muga ana yin noma har zuwa gazayowar wata daminar a jihar, musamman domin al’ummarmu su kasance cikin shiri wajen gudanar da ayyuka a koda-yaushe tare kuma da amfana daga kudaden da aka kashe wajen sake gyaran wannan Dam da aka yi watsi da shi a baya”, a cewar gwamnan.

Shi kuwa a nasa bangaren, wakilin OCP na Afirka; Alik Orebaoghene ya sanar da cewa; gonar za ta kasance wajen bayar da horon sanin makamar aikin noma, musamman a tsakanin kananan manoma da ke jihar.

A karkashin wannan hadaka, ana sa ran OCP na Afirka zai samar da ingantaccen takin zamanin da za a gudanar da wannan aiki.

Shi ma, Manajan Daraktan Hukumar SRRBDA; ‎Abubakar Malam, a nasa jawabin, jinjina ya yi kan kokarin da aka yi na sake farfado da wannan aiki.

Ya sanar da cewa, bisa tsarin kudurin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu (Renewed Hope Agenda), muna alfahari da samar da hektar noma daidai har guda 50, domin aiwatar da wannan aiki; musamman domin kara samar da wadataccen abinci a wannan kasa.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

Next Post

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

4 days ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

4 days ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: 'Yansandan Indiya Sun Kama 'Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

September 10, 2025
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

September 10, 2025
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.