• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Awannin Da Sallamarsu A Matsayin Kwamishinoni, Gwamnan Bauchi Ya Naɗa 3 A Matsayin Mashawarta

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
10 months ago
Bala Mohammed

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya naɗa uku daga cikin Kwamishinoni biyar da ya sallama daga muƙamansu a matsayin manyan masu ba shi shawara a ɓangarori daban-daban. 

 

Idan za ku tuna dai mun labarto cewa gwamnan da safiyar ranar Talata ya sallami Kwamishinonin guda biyar da suka haɗa da: Dakta Jamila Mohammed Dahiru – daga ma’aikatar ilimi; Barista Abubakar Abdulhameed Bununu – Tsoron Cikin Gida; Kwamared Usman Danturaki wanda aka kora a matsayin Kwamishinan watsa labarai; Farfesa Simon Madugu Yalams – Ayyukan Gona sai kuma Kwamishina a ma’aikatar harkokin addinai, Alhaji Yakubu Ibrahim Hamza

  • Hatsarin Kwale-kwale: Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya Ta Ceto Jami’an ‘Yansanda 8 Da Wani A Bayelsa
  • Adadin Kudin Ajiyar Sin Na Ketare Ya Ragu Zuwa Dala Tiriliyan 3.2024

Sai dai awannin da wannan matakin, gwamnan ya naɗa uku daga cikinsu a matsayin manyan Mashawarta domin su ci gaba da amfani da gogewarsu wajen taimaka wa gwamnatin jihar a ɓangaren gudanar da harkokin mulki.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Sabbin waɗanda gwamnan ya naɗa a matsayin manyan masu ba shi shawara sun ƙunshi, Hon. Abubakar Abdulhameed Bununu – babban mashawarci a ɓangaren haɗa kan jama’a da yankuna; Kwamared Usman Danturaki – mashawarci kan harkokin kwadago da shirin taimakekeniyar Fansho yayin da lima Farfesa Simon Madugu Yalams – Mashawarcin kan fasaha da ilimin koyon sana’ar hannu.

 

A wata sanarwar da mai magana da yawun gwamnan jihar, Mukhtar Mohammed Gidado ya fitar a daren ranar Talata, ya ce, naɗe-naɗen da suka fara aiki nan take an yi ne da nufin gwamnan na kyautata shugabanci da janyo kowa a jika haɗi da muradun cimma nasarori kan burikan gwamnati mai ci.

 

Gwamnan ya hori sabbin waɗanda ya naɗan da su yi amfani da gogewarsu da ƙwarewarsu wajen ba da tasu gudunmawar wajen cimma kyawawan ayyukan raya jihar. Kana, ya nemi su yi aiki tsakani da Allah domin kyautata rayuwar al’ummar jihar Bauchi.

 

Gwamnan ya jaddada aniyarsa na tabbatar da gaskiya da rikon amana hadi da gudanar da mulki na kowa da kowa domin ciyar da jihar zuwa gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina
Labarai

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Next Post
Éric Chelle Ya Zama Sabon Kocin Super Eagles

Éric Chelle Ya Zama Sabon Kocin Super Eagles

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
Bauchi

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.