ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Awannin Da Sallamarsu A Matsayin Kwamishinoni, Gwamnan Bauchi Ya Naɗa 3 A Matsayin Mashawarta

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
10 months ago
Bala Mohammed

Gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad ya naɗa uku daga cikin Kwamishinoni biyar da ya sallama daga muƙamansu a matsayin manyan masu ba shi shawara a ɓangarori daban-daban. 

 

Idan za ku tuna dai mun labarto cewa gwamnan da safiyar ranar Talata ya sallami Kwamishinonin guda biyar da suka haɗa da: Dakta Jamila Mohammed Dahiru – daga ma’aikatar ilimi; Barista Abubakar Abdulhameed Bununu – Tsoron Cikin Gida; Kwamared Usman Danturaki wanda aka kora a matsayin Kwamishinan watsa labarai; Farfesa Simon Madugu Yalams – Ayyukan Gona sai kuma Kwamishina a ma’aikatar harkokin addinai, Alhaji Yakubu Ibrahim Hamza

ADVERTISEMENT
  • Hatsarin Kwale-kwale: Rundunar Sojin Ruwan Nijeriya Ta Ceto Jami’an ‘Yansanda 8 Da Wani A Bayelsa
  • Adadin Kudin Ajiyar Sin Na Ketare Ya Ragu Zuwa Dala Tiriliyan 3.2024

Sai dai awannin da wannan matakin, gwamnan ya naɗa uku daga cikinsu a matsayin manyan Mashawarta domin su ci gaba da amfani da gogewarsu wajen taimaka wa gwamnatin jihar a ɓangaren gudanar da harkokin mulki.

 

LABARAI MASU NASABA

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Sabbin waɗanda gwamnan ya naɗa a matsayin manyan masu ba shi shawara sun ƙunshi, Hon. Abubakar Abdulhameed Bununu – babban mashawarci a ɓangaren haɗa kan jama’a da yankuna; Kwamared Usman Danturaki – mashawarci kan harkokin kwadago da shirin taimakekeniyar Fansho yayin da lima Farfesa Simon Madugu Yalams – Mashawarcin kan fasaha da ilimin koyon sana’ar hannu.

 

A wata sanarwar da mai magana da yawun gwamnan jihar, Mukhtar Mohammed Gidado ya fitar a daren ranar Talata, ya ce, naɗe-naɗen da suka fara aiki nan take an yi ne da nufin gwamnan na kyautata shugabanci da janyo kowa a jika haɗi da muradun cimma nasarori kan burikan gwamnati mai ci.

 

Gwamnan ya hori sabbin waɗanda ya naɗan da su yi amfani da gogewarsu da ƙwarewarsu wajen ba da tasu gudunmawar wajen cimma kyawawan ayyukan raya jihar. Kana, ya nemi su yi aiki tsakani da Allah domin kyautata rayuwar al’ummar jihar Bauchi.

 

Gwamnan ya jaddada aniyarsa na tabbatar da gaskiya da rikon amana hadi da gudanar da mulki na kowa da kowa domin ciyar da jihar zuwa gaba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,
Kasashen Ketare

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Next Post
Éric Chelle Ya Zama Sabon Kocin Super Eagles

Éric Chelle Ya Zama Sabon Kocin Super Eagles

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.