• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu

by Idris Aliyu Daudawa
8 months ago
in Ilimi
0
Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’an ilimi kwararru ne a bangaren ilimi wanda aikinsu shi ne da alhakin bunkasawa, aiwatarwa,da kuma tsara manufofin ilimi da tsare tsare.Suna bada gudunmawa wajen tabbatar da cewa kowa yana samun ingantaccen ilimi mai nagarta. Jami’an ilimi sune yin aiki ne a wurare daban- daban da suka hada da hukumomin gwamnati, wuraren ko hukumomin da ba a kafa su saboda su samar da riba da kuma makarantun ilimi. Gudunmuwoyin  da jami’an ilimi suke badawa suna da yawa.

Suke da alhakin shirya bincike da kuma nazari domin su gano wuraren da suke da matsalolin da suka shafi ilimi, da kuma samar da hanyoyin da za ayi maganinsu. Hakanan ma jami’an ilimi suna samar da shawarar data kamata da kuma taimako ga Malamai da sauran masu harkar data shafi ilimi domin tabbatar da cewa suna bada nagartaccen ilimi ga dalibai.

  • Kidayar Jama’a Da Harkar Ilimi
  • Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Kudin Shiga Na Naira Tirililan 34.8 A 2025

Bugu da kari suna kuma taimakawa wajen samar da yadda za a tafiyar da lamari, tsara shi, da yadda za a gabatar horarwa,da rika bibiyar yadda ake aiwatar da duk wani taimakon da ake ba ilimi.Wannan ya hada bayan aikin su Malamai da kuma masana ilimi, jami’an ilimi har ila yau suna mu’amala da Malamai, dalibai da sauran masu ruwa da tsaki ta bangaren ilim.

 

Suna aiki domin su kulla dankon zumunci da hadin gwiwa domin tabbatar da cewar ana biyan duk bukataun kowa. Hakanan ma su jami’an ilimin suna bada gudunmawa wajen  bibiyar yadda ake aiwatar da tsare- tsare da manufofin ilimi kamar yadda ya dace. Suna amfani ne da fasahar zamani da sauran wasu abubuwan da suka zama sheda domin gano wuraren da suke da bukatar da a kawo masu dauki, da daukar matakan da za su samar da canji.Maganar gaskiya jami’an ilimi suna da muhimmanci saboda tabbatar da kowa ya samu ilimi, babu bambanci mai kuma inganci.Ayyukansu na taimakawa wajen yadda ilimi zai iya kasancewa a gaba da kuma tabbatar da cewa dalibai sun samu  mizanin ilimin daya dace su samu.Duk hakan na kasancewa ta wajen samar da yadda ya dace a tafiyar da lamari, taimakawa, da jagoranci, jami’an  ilimi har ila yau suna samar da yanayi maikyu da yake bunkasa koyon ilimi ga masu koyo da ke koyawa ilimin. Digiri satifiket na shedar Ilimin ya kamata ace jami’in ilimi ya mallaka

Labarai Masu Nasaba

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

 

Jami’in ilimi mutum ne wanda alhakin kulawa da ilimi ake aiwatar da shi tare da dukkan tsare- tsare ko manufofi suka  rataya a wuyansa, ko dai a wata hukuma ko kuma wurin da al’umma suke. Idan mutum na bukatar zama jami’in ilimi akwai bukatar ace  ya mallaki takardar shedar ilimi.Ko kuma a kalla yana da digiri na farko a sashen da ya shafi ilimi. Duk da hakan ma ana bukatar da yana da kwarewa ko ya taba aikin koyarwa ko kuma ilimin da yake da alaka da tafiyar da harkar mulki ya kan zama dole hakan. Idan ana maganar dabara kuma jami’in ilimi abin so ne ace ya mallaki ko yana da dabarar iya hulda da al’umma kwarai da gaske, domin kuwa zai rika hulda ne da mutane daban- daban da suka hada da Malamai, dalibai, Iyaye,da sauran masu fada aji ta bangaren  ilimi.Akwai bukatar su kasance sun san makamar tafiyar da manufofin ilimi da yadda za a aiwatar da su,da kuma samun mafita daga wasu.Su kasance sun nakalci da sanin yadda za a tafiyar da harkokin ilimi sosai.Ga kuma su iya tafiyar da ayyukan kan lokacin da aka ce masu,kai hara ma da su bunkasa da kuma tsare- tsare da manufofin ilimi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ilimi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Sin Ya Yi Tir Da Harin Isra’ila Kan Cibiyoyin Kiwon Lafiya A Gaza

Next Post

Ko Me Ya Sa Amurka Ta Gaza Cimma Burinta Na Yakin Kimiyya Da Fasaha Da Kasar Sin?

Related

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima
Ilimi

Kungiyoyi Masu Fada Aji Kan Harkar Ilimi Sun Nemi A Yi Wa Sashen Kwaskwarima

6 days ago
Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah
Ilimi

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah

2 weeks ago
Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya
Ilimi

Kwamitin Tantance Makarantun Gaba da Sakandire Na Bogi Ya Yi Wa Yankin Funtua Dirar Mikiya

3 weeks ago
Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

4 weeks ago
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
Ilimi

‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

1 month ago
UTME
Ilimi

An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

1 month ago
Next Post
Ko Me Ya Sa Amurka Ta Gaza Cimma Burinta Na Yakin Kimiyya Da Fasaha Da Kasar Sin?

Ko Me Ya Sa Amurka Ta Gaza Cimma Burinta Na Yakin Kimiyya Da Fasaha Da Kasar Sin?

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.