• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu

by Idris Aliyu Daudawa
10 months ago
ilimi

Jami’an ilimi kwararru ne a bangaren ilimi wanda aikinsu shi ne da alhakin bunkasawa, aiwatarwa,da kuma tsara manufofin ilimi da tsare tsare.Suna bada gudunmawa wajen tabbatar da cewa kowa yana samun ingantaccen ilimi mai nagarta. Jami’an ilimi sune yin aiki ne a wurare daban- daban da suka hada da hukumomin gwamnati, wuraren ko hukumomin da ba a kafa su saboda su samar da riba da kuma makarantun ilimi. Gudunmuwoyin  da jami’an ilimi suke badawa suna da yawa.

Suke da alhakin shirya bincike da kuma nazari domin su gano wuraren da suke da matsalolin da suka shafi ilimi, da kuma samar da hanyoyin da za ayi maganinsu. Hakanan ma jami’an ilimi suna samar da shawarar data kamata da kuma taimako ga Malamai da sauran masu harkar data shafi ilimi domin tabbatar da cewa suna bada nagartaccen ilimi ga dalibai.

  • Kidayar Jama’a Da Harkar Ilimi
  • Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Kudin Shiga Na Naira Tirililan 34.8 A 2025

Bugu da kari suna kuma taimakawa wajen samar da yadda za a tafiyar da lamari, tsara shi, da yadda za a gabatar horarwa,da rika bibiyar yadda ake aiwatar da duk wani taimakon da ake ba ilimi.Wannan ya hada bayan aikin su Malamai da kuma masana ilimi, jami’an ilimi har ila yau suna mu’amala da Malamai, dalibai da sauran masu ruwa da tsaki ta bangaren ilim.

 

Suna aiki domin su kulla dankon zumunci da hadin gwiwa domin tabbatar da cewar ana biyan duk bukataun kowa. Hakanan ma su jami’an ilimin suna bada gudunmawa wajen  bibiyar yadda ake aiwatar da tsare- tsare da manufofin ilimi kamar yadda ya dace. Suna amfani ne da fasahar zamani da sauran wasu abubuwan da suka zama sheda domin gano wuraren da suke da bukatar da a kawo masu dauki, da daukar matakan da za su samar da canji.Maganar gaskiya jami’an ilimi suna da muhimmanci saboda tabbatar da kowa ya samu ilimi, babu bambanci mai kuma inganci.Ayyukansu na taimakawa wajen yadda ilimi zai iya kasancewa a gaba da kuma tabbatar da cewa dalibai sun samu  mizanin ilimin daya dace su samu.Duk hakan na kasancewa ta wajen samar da yadda ya dace a tafiyar da lamari, taimakawa, da jagoranci, jami’an  ilimi har ila yau suna samar da yanayi maikyu da yake bunkasa koyon ilimi ga masu koyo da ke koyawa ilimin. Digiri satifiket na shedar Ilimin ya kamata ace jami’in ilimi ya mallaka

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

 

Jami’in ilimi mutum ne wanda alhakin kulawa da ilimi ake aiwatar da shi tare da dukkan tsare- tsare ko manufofi suka  rataya a wuyansa, ko dai a wata hukuma ko kuma wurin da al’umma suke. Idan mutum na bukatar zama jami’in ilimi akwai bukatar ace  ya mallaki takardar shedar ilimi.Ko kuma a kalla yana da digiri na farko a sashen da ya shafi ilimi. Duk da hakan ma ana bukatar da yana da kwarewa ko ya taba aikin koyarwa ko kuma ilimin da yake da alaka da tafiyar da harkar mulki ya kan zama dole hakan. Idan ana maganar dabara kuma jami’in ilimi abin so ne ace ya mallaki ko yana da dabarar iya hulda da al’umma kwarai da gaske, domin kuwa zai rika hulda ne da mutane daban- daban da suka hada da Malamai, dalibai, Iyaye,da sauran masu fada aji ta bangaren  ilimi.Akwai bukatar su kasance sun san makamar tafiyar da manufofin ilimi da yadda za a aiwatar da su,da kuma samun mafita daga wasu.Su kasance sun nakalci da sanin yadda za a tafiyar da harkokin ilimi sosai.Ga kuma su iya tafiyar da ayyukan kan lokacin da aka ce masu,kai hara ma da su bunkasa da kuma tsare- tsare da manufofin ilimi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
ASUU
Ilimi

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Next Post
Ko Me Ya Sa Amurka Ta Gaza Cimma Burinta Na Yakin Kimiyya Da Fasaha Da Kasar Sin?

Ko Me Ya Sa Amurka Ta Gaza Cimma Burinta Na Yakin Kimiyya Da Fasaha Da Kasar Sin?

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.