• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (3)

by Idris Aliyu Daudawa
9 months ago
Ilimi

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Jami’an ilimi kwararru ne wadanda suke bada muhimmiyar gudunmawa wajen ci gaban makarantun ilimi,wajen tabbatar da cewar suna bin matakan ilimin da gwamnati ta amince ayi amfani da su.

Ayyukan jami’an ilimi sun sha bamban wannan kuma ya danganta ne da irin nau’in ilimin,amma babban aikinsu shi ne su kasance masu lura da yadda abubuwa suke tafiya tsakanin gwamnati da makarantu.

  • Kauyuka Suna Kokarin Neman Cimma Burin Samun Wadata Tare A Kasar Sin
  • Duniya Na Fatan Sin Da Amurka Za Su Cika Alkawuransu Cikin Hadin Gwiwa

Suna tabbatar da cewa makarantu suna suna bin dokoki da tsare- tsare wadanda gamwnati ta ce sai an yi amfan da su,inda za su rika bin diddiki na sanin yadda abubuwa suke ta hanyar byin ziyarce- ziyarcen makarantun.Jami’an ilimi sune ke da alhakin tabbatar da cewa makarantu suna da isassun Malamai, kayan koyarwa, da kuma isassun abubuwan da za su taimaka wajen samar da nagartaccen ilimi.  Suna aiki ne domin su inganta nagartar ilimi wajen samar da Malamai da kuma dukkan hore- horen da suka dace da kuma taimakon da ake bukata domin a samu bunkasa ilimi ta hanyar samar da Malamai da dukkan hore- horen inganta ilimi da suka kamata ayi masu domin tabbatar da ana samar da ingantaccen ilimi ga dalibai masu neman ilimi. Jami’an ilimi suna yin aiki da jami’an hukumomin makarantu domin su samar da tsare- tsare da ke sanadiyar jin dadin dalibai,da kuma inganta gaba dayan yadda ko inganta yadda koyarwa za ta jawo hankalin dalibai.Jami’an iimi har ila yau sune ke da alhakin nazarin yadda kwazo, fahimta,ko gane abubwan da ake koyawa dalibai suna tafiya kamar yadda ya dace,suna tabbatar da su daliban suna yin abin da ake bukata da ya shafi ilimin su. Suna yin aiki kafada- kafada da Malamai wajen samar da muradan koyarwa masu kyau da za su taimakawa dalibai cimma burinsu na karatu.Hakanan ma jami’an ilimi suna kokarin irin daliban da basu gane abubuwan da aka koya masu ba kamar yadda ake so,ta haka kuma za su taimaka masu da dukkanin abubuwan da suka kamata, da za su taimaka ma su kara kwazon su.Daga karshe jami’an ilimi kwararru ne masu matukar amfani wadanda burinsu bai wuce tabbatar da makarantu suna samar/ bada ilimi mai nagarta ga dalibai.Suna aiki domin tabbatar da makarantu  suna aiki da dokoki, tsare- tsare, kula da jin dadin dalibai, da kuma inganta gaba dayan abubuwan da suke bunkasa koyarwa da gane darussan da ake koyawa kamar yadda ya dace.Bugu da kari jami’an ilimi suna aiki tare da Malamai domin su samar da hanyoyin koyarwa ga Malamai wadanda suma kansu hakan zai taimaka masu taimakawa daliban da suke da matsalar gane abubuwan da ake koya masu.

Jami’an ilimi wasu kwararru ne da suke da alhakin lura da yadda ake tafiyar da harkokin ilimi da ganin  al’amura na tafiya kamar yadda ya dace su kasance musamman ma a hukuma.Suna ayyuka da suka sha bamban da juna amma duk muradan daya ne kamar a makarantu, Kwalejoji,da kuma Jami’oi, da sauran makarantu inda ake harkar ilimi.Ayyukan jami’an ilimi sun sha bamban wannan kuma ya danganta ne ga irin hukumar da suke yi wa aiki, sai dai abinda aka fi sani sune masu samar da tsare- tsaren ilimi da kuma aiwatar da su gwargwadon yadda su muradan hukumar ko ita makarantar. Suna ma tabbatar da cewa su manhajojin da yadda ake koyawa dalibai hakan ya yi dai dai da irin mizanin da ake son cimmawa kan yadda dokoki suka amince da ayi. Abin na su bai tsaya anan ba domin kuwa har ma suna kafada-kafada da Malamai, jami’an makaranta,da sauran ma’aikatan wurin domin a gano wuraren da ake bukatar a maida hankali na lamarin da ya shafi tafarkin ilimin.Suna samar da horo da ci gaban kwarewa tare da samar da wata kafa ga Malamai, abin bai tsaya kan su ba kadai, domin kuwa har ma da dalibai, wadanda watakila suna da bukatar wani karin haske dangane da abubuwan da ake koya ma su

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba
Ilimi

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi
Ilimi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta
Ilimi

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Next Post
Babu Dalilin Fargaba Ko Tsoro Don Sanya Wa Mara Lafiya Robar Hanci

Babu Dalilin Fargaba Ko Tsoro Don Sanya Wa Mara Lafiya Robar Hanci

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.