• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon yin azumi a lokacin bazara da kuma karancin wutar lantar a Nijeriya ya sa ‘yan kasuwar kankara ke camamarsu a bana.
A Jihohin Borno da Yobe suna daga ciki bangarorin kasar nan da ke gaba-gaba a tsananin zafin rana, sakamakon yadda suke da adadin murabba’in daruruwan kil-omitoci da sahara ta mamaye a Arewa Maso Gabashin Nijeriya kuma sun yi iyaka da Jamhuriyar Nijar, Chadi da Kamaru.

Yanayin zafin ranar yankin ya bambanta da na sauran yankuna tare da guguwa mai dauke da iska mai zafi a lokacin bazara. Haka zalika, yanki ne mai karancin bishiyoyi masu inuwar da mutum zai sarara, face kebantattun wuraren da suke gabar Kogin Kumadugu da makamantan sa.

  • Ce-ce-ku-ce Ya Barke Tsakanin PDP Da APC Kan Zargin Kama Mambobi 25 A Osun
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Benin Domin Tattauna Hanyoyin Karfafa Dangantakar Kasashensu

Yanki ne wanda sakamakon matsalolin tsaron da ya sha fama da su, har yanzu al’ummar yankin ba su kammala fita daga cikin tasku da matsin rayuwa da rikicin Boko Haram ya jefa su a ciki ba. Al’amarin da ya shafi kusan kowane fannin jin dadin rayuwa, inda maharan suka rinka rusa manyan layukan wutar lantarkin da ya sada manyan biranen jihohin Maiduguri da Damaturu ba su da lantarki.

Bugu da kari, birnin Maiduguri ya kwashe watanni ba tare da wutar lantarki ba, sakamakon ayyukan ‘yan kungiyar Boko Haram da suka katse manyan layukan wutar lantarki tun a bara, duk da matakin da gwamnati ta dauka na gyara amma dai ba ta canja zani ba.

Haka abin yake a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, wanda a cikin kasa ga katanni hudu, Boko Haram sun katse layukan wutar lantarkin da ke baiwa jihohin biyu wutar lantarki a kauye Kasesa dake daf da Damaturu.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Wadannan sun jawo samun ruwan sanyi ko kankara don sanyaya makoshin masu azumi ya wuyata. Wanda hakan ya jawo tsadar kankara tare da sauran abu-buwan sanyi wadanda mai azumi yake bukata domin sanyaya makoshi a lokacin buda baki.
Jama’a da dama sun shaida wa LEADERSHIP cewa yanzu haka su na sanyen kankarar ‘Pure Water’ daya kan 200 ko 150 a wadannan manyan garuruwa da makamantan su.

Malama Fatima Mustapha, mazuniyar birnin Maiduguri ta bayyana cewa, “Tun shigowar azumin haka muke ta fama da tsananin zafi sakamakon rashin wutar lantarki, wanda tun bayan shigowar watan Ramadan ba mu samu isasshen wutan ba, alhalin ga azumi ga tsanain zafin da ake da shi a nan Borno.

“Wanda hakan ya tilasta dole sai mutum ya yi tafiya mai nisa zuwa wasu ungu-wanni kafin ya samu kankara, kowace ake sayar da ledar Pure water daya kan 200. Sannan ga yanayin matsin rayuwa.”

A nashi bangaren kuma, Malam Abubakar Usman Damaturu, ya bayyana cewa rashin samun isasshen wutar lantarki a birnin shi ne ummul-haba’isan tsadar kankara tare da sauran kayan masarufi.

“Mafi yawan kankarar ana kawota ne daga Potiskum, wanda a farkon azumi kowace daya 500 ce (ba ta pure water ba). Sannan kuma zancen wutar lantarki kam sai dai mu ce Alhamdulillah.” In ji shi.

A Jihar Zamfara ma haka lamarin yake, domin kuwa al’ummar Jihar Zamfara al’umar na matukar shan wahala a wannan azumi wajen sanyaya makoshi a loka-cin buda baki.
Wannan ne ya sanya wasu su ka yi wa sana’ar sayar da kankara kutse ganin yad-da farashin ke hauhawa, musamman a Gusau babban birnin Jihar Zamfara.

Hamza Zurmi ya bayyana wa wakilinmu cewa, dafifi magidajan ke yi wajen sayan kakara ga layi mai tsawo duk da kuwa ba kowane yake samun yadda yake soba.

A yankin Janyau ta gabas da Samaru Gusau, a wani ashirin da hudu suke yi kan samun wuta lantarki, inda ake matukar shan wahala tare tsadar wajen sayen kankara.

Masu sayar da kankara a azumin bana sun yi camamarsu a mafi yawancin yankunan kasar nan sakamakon tsananin zafi da kuma rashin samun isasshin wutar lantarki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jimilar Kudin Da Sin Ta Samu Wajen Jigilar Kayayyaki A Farkon Watanni Biyu Na Bana Ta Kai Yuan Triliyan 55.4

Next Post

Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

2 hours ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

3 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

5 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

7 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

9 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

10 hours ago
Next Post
Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.