ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara

by Sulaiman
2 years ago
Kankara

Sakamakon yin azumi a lokacin bazara da kuma karancin wutar lantar a Nijeriya ya sa ‘yan kasuwar kankara ke camamarsu a bana.
A Jihohin Borno da Yobe suna daga ciki bangarorin kasar nan da ke gaba-gaba a tsananin zafin rana, sakamakon yadda suke da adadin murabba’in daruruwan kil-omitoci da sahara ta mamaye a Arewa Maso Gabashin Nijeriya kuma sun yi iyaka da Jamhuriyar Nijar, Chadi da Kamaru.

Yanayin zafin ranar yankin ya bambanta da na sauran yankuna tare da guguwa mai dauke da iska mai zafi a lokacin bazara. Haka zalika, yanki ne mai karancin bishiyoyi masu inuwar da mutum zai sarara, face kebantattun wuraren da suke gabar Kogin Kumadugu da makamantan sa.

  • Ce-ce-ku-ce Ya Barke Tsakanin PDP Da APC Kan Zargin Kama Mambobi 25 A Osun
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Benin Domin Tattauna Hanyoyin Karfafa Dangantakar Kasashensu

Yanki ne wanda sakamakon matsalolin tsaron da ya sha fama da su, har yanzu al’ummar yankin ba su kammala fita daga cikin tasku da matsin rayuwa da rikicin Boko Haram ya jefa su a ciki ba. Al’amarin da ya shafi kusan kowane fannin jin dadin rayuwa, inda maharan suka rinka rusa manyan layukan wutar lantarkin da ya sada manyan biranen jihohin Maiduguri da Damaturu ba su da lantarki.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, birnin Maiduguri ya kwashe watanni ba tare da wutar lantarki ba, sakamakon ayyukan ‘yan kungiyar Boko Haram da suka katse manyan layukan wutar lantarki tun a bara, duk da matakin da gwamnati ta dauka na gyara amma dai ba ta canja zani ba.

Haka abin yake a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, wanda a cikin kasa ga katanni hudu, Boko Haram sun katse layukan wutar lantarkin da ke baiwa jihohin biyu wutar lantarki a kauye Kasesa dake daf da Damaturu.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Wadannan sun jawo samun ruwan sanyi ko kankara don sanyaya makoshin masu azumi ya wuyata. Wanda hakan ya jawo tsadar kankara tare da sauran abu-buwan sanyi wadanda mai azumi yake bukata domin sanyaya makoshi a lokacin buda baki.
Jama’a da dama sun shaida wa LEADERSHIP cewa yanzu haka su na sanyen kankarar ‘Pure Water’ daya kan 200 ko 150 a wadannan manyan garuruwa da makamantan su.

Malama Fatima Mustapha, mazuniyar birnin Maiduguri ta bayyana cewa, “Tun shigowar azumin haka muke ta fama da tsananin zafi sakamakon rashin wutar lantarki, wanda tun bayan shigowar watan Ramadan ba mu samu isasshen wutan ba, alhalin ga azumi ga tsanain zafin da ake da shi a nan Borno.

“Wanda hakan ya tilasta dole sai mutum ya yi tafiya mai nisa zuwa wasu ungu-wanni kafin ya samu kankara, kowace ake sayar da ledar Pure water daya kan 200. Sannan ga yanayin matsin rayuwa.”

A nashi bangaren kuma, Malam Abubakar Usman Damaturu, ya bayyana cewa rashin samun isasshen wutar lantarki a birnin shi ne ummul-haba’isan tsadar kankara tare da sauran kayan masarufi.

“Mafi yawan kankarar ana kawota ne daga Potiskum, wanda a farkon azumi kowace daya 500 ce (ba ta pure water ba). Sannan kuma zancen wutar lantarki kam sai dai mu ce Alhamdulillah.” In ji shi.

A Jihar Zamfara ma haka lamarin yake, domin kuwa al’ummar Jihar Zamfara al’umar na matukar shan wahala a wannan azumi wajen sanyaya makoshi a loka-cin buda baki.
Wannan ne ya sanya wasu su ka yi wa sana’ar sayar da kankara kutse ganin yad-da farashin ke hauhawa, musamman a Gusau babban birnin Jihar Zamfara.

Hamza Zurmi ya bayyana wa wakilinmu cewa, dafifi magidajan ke yi wajen sayan kakara ga layi mai tsawo duk da kuwa ba kowane yake samun yadda yake soba.

A yankin Janyau ta gabas da Samaru Gusau, a wani ashirin da hudu suke yi kan samun wuta lantarki, inda ake matukar shan wahala tare tsadar wajen sayen kankara.

Masu sayar da kankara a azumin bana sun yi camamarsu a mafi yawancin yankunan kasar nan sakamakon tsananin zafi da kuma rashin samun isasshin wutar lantarki.

Kankara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.