• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon yin azumi a lokacin bazara da kuma karancin wutar lantar a Nijeriya ya sa ‘yan kasuwar kankara ke camamarsu a bana.
A Jihohin Borno da Yobe suna daga ciki bangarorin kasar nan da ke gaba-gaba a tsananin zafin rana, sakamakon yadda suke da adadin murabba’in daruruwan kil-omitoci da sahara ta mamaye a Arewa Maso Gabashin Nijeriya kuma sun yi iyaka da Jamhuriyar Nijar, Chadi da Kamaru.

Yanayin zafin ranar yankin ya bambanta da na sauran yankuna tare da guguwa mai dauke da iska mai zafi a lokacin bazara. Haka zalika, yanki ne mai karancin bishiyoyi masu inuwar da mutum zai sarara, face kebantattun wuraren da suke gabar Kogin Kumadugu da makamantan sa.

  • Ce-ce-ku-ce Ya Barke Tsakanin PDP Da APC Kan Zargin Kama Mambobi 25 A Osun
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Benin Domin Tattauna Hanyoyin Karfafa Dangantakar Kasashensu

Yanki ne wanda sakamakon matsalolin tsaron da ya sha fama da su, har yanzu al’ummar yankin ba su kammala fita daga cikin tasku da matsin rayuwa da rikicin Boko Haram ya jefa su a ciki ba. Al’amarin da ya shafi kusan kowane fannin jin dadin rayuwa, inda maharan suka rinka rusa manyan layukan wutar lantarkin da ya sada manyan biranen jihohin Maiduguri da Damaturu ba su da lantarki.

Bugu da kari, birnin Maiduguri ya kwashe watanni ba tare da wutar lantarki ba, sakamakon ayyukan ‘yan kungiyar Boko Haram da suka katse manyan layukan wutar lantarki tun a bara, duk da matakin da gwamnati ta dauka na gyara amma dai ba ta canja zani ba.

Haka abin yake a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, wanda a cikin kasa ga katanni hudu, Boko Haram sun katse layukan wutar lantarkin da ke baiwa jihohin biyu wutar lantarki a kauye Kasesa dake daf da Damaturu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Wadannan sun jawo samun ruwan sanyi ko kankara don sanyaya makoshin masu azumi ya wuyata. Wanda hakan ya jawo tsadar kankara tare da sauran abu-buwan sanyi wadanda mai azumi yake bukata domin sanyaya makoshi a lokacin buda baki.
Jama’a da dama sun shaida wa LEADERSHIP cewa yanzu haka su na sanyen kankarar ‘Pure Water’ daya kan 200 ko 150 a wadannan manyan garuruwa da makamantan su.

Malama Fatima Mustapha, mazuniyar birnin Maiduguri ta bayyana cewa, “Tun shigowar azumin haka muke ta fama da tsananin zafi sakamakon rashin wutar lantarki, wanda tun bayan shigowar watan Ramadan ba mu samu isasshen wutan ba, alhalin ga azumi ga tsanain zafin da ake da shi a nan Borno.

“Wanda hakan ya tilasta dole sai mutum ya yi tafiya mai nisa zuwa wasu ungu-wanni kafin ya samu kankara, kowace ake sayar da ledar Pure water daya kan 200. Sannan ga yanayin matsin rayuwa.”

A nashi bangaren kuma, Malam Abubakar Usman Damaturu, ya bayyana cewa rashin samun isasshen wutar lantarki a birnin shi ne ummul-haba’isan tsadar kankara tare da sauran kayan masarufi.

“Mafi yawan kankarar ana kawota ne daga Potiskum, wanda a farkon azumi kowace daya 500 ce (ba ta pure water ba). Sannan kuma zancen wutar lantarki kam sai dai mu ce Alhamdulillah.” In ji shi.

A Jihar Zamfara ma haka lamarin yake, domin kuwa al’ummar Jihar Zamfara al’umar na matukar shan wahala a wannan azumi wajen sanyaya makoshi a loka-cin buda baki.
Wannan ne ya sanya wasu su ka yi wa sana’ar sayar da kankara kutse ganin yad-da farashin ke hauhawa, musamman a Gusau babban birnin Jihar Zamfara.

Hamza Zurmi ya bayyana wa wakilinmu cewa, dafifi magidajan ke yi wajen sayan kakara ga layi mai tsawo duk da kuwa ba kowane yake samun yadda yake soba.

A yankin Janyau ta gabas da Samaru Gusau, a wani ashirin da hudu suke yi kan samun wuta lantarki, inda ake matukar shan wahala tare tsadar wajen sayen kankara.

Masu sayar da kankara a azumin bana sun yi camamarsu a mafi yawancin yankunan kasar nan sakamakon tsananin zafi da kuma rashin samun isasshin wutar lantarki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jimilar Kudin Da Sin Ta Samu Wajen Jigilar Kayayyaki A Farkon Watanni Biyu Na Bana Ta Kai Yuan Triliyan 55.4

Next Post

Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

Related

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

2 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

3 hours ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

10 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

10 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

13 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

14 hours ago
Next Post
Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.