ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara

by Sulaiman
2 years ago
Kankara

Sakamakon yin azumi a lokacin bazara da kuma karancin wutar lantar a Nijeriya ya sa ‘yan kasuwar kankara ke camamarsu a bana.
A Jihohin Borno da Yobe suna daga ciki bangarorin kasar nan da ke gaba-gaba a tsananin zafin rana, sakamakon yadda suke da adadin murabba’in daruruwan kil-omitoci da sahara ta mamaye a Arewa Maso Gabashin Nijeriya kuma sun yi iyaka da Jamhuriyar Nijar, Chadi da Kamaru.

Yanayin zafin ranar yankin ya bambanta da na sauran yankuna tare da guguwa mai dauke da iska mai zafi a lokacin bazara. Haka zalika, yanki ne mai karancin bishiyoyi masu inuwar da mutum zai sarara, face kebantattun wuraren da suke gabar Kogin Kumadugu da makamantan sa.

  • Ce-ce-ku-ce Ya Barke Tsakanin PDP Da APC Kan Zargin Kama Mambobi 25 A Osun
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Benin Domin Tattauna Hanyoyin Karfafa Dangantakar Kasashensu

Yanki ne wanda sakamakon matsalolin tsaron da ya sha fama da su, har yanzu al’ummar yankin ba su kammala fita daga cikin tasku da matsin rayuwa da rikicin Boko Haram ya jefa su a ciki ba. Al’amarin da ya shafi kusan kowane fannin jin dadin rayuwa, inda maharan suka rinka rusa manyan layukan wutar lantarkin da ya sada manyan biranen jihohin Maiduguri da Damaturu ba su da lantarki.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, birnin Maiduguri ya kwashe watanni ba tare da wutar lantarki ba, sakamakon ayyukan ‘yan kungiyar Boko Haram da suka katse manyan layukan wutar lantarki tun a bara, duk da matakin da gwamnati ta dauka na gyara amma dai ba ta canja zani ba.

Haka abin yake a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, wanda a cikin kasa ga katanni hudu, Boko Haram sun katse layukan wutar lantarkin da ke baiwa jihohin biyu wutar lantarki a kauye Kasesa dake daf da Damaturu.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Wadannan sun jawo samun ruwan sanyi ko kankara don sanyaya makoshin masu azumi ya wuyata. Wanda hakan ya jawo tsadar kankara tare da sauran abu-buwan sanyi wadanda mai azumi yake bukata domin sanyaya makoshi a lokacin buda baki.
Jama’a da dama sun shaida wa LEADERSHIP cewa yanzu haka su na sanyen kankarar ‘Pure Water’ daya kan 200 ko 150 a wadannan manyan garuruwa da makamantan su.

Malama Fatima Mustapha, mazuniyar birnin Maiduguri ta bayyana cewa, “Tun shigowar azumin haka muke ta fama da tsananin zafi sakamakon rashin wutar lantarki, wanda tun bayan shigowar watan Ramadan ba mu samu isasshen wutan ba, alhalin ga azumi ga tsanain zafin da ake da shi a nan Borno.

“Wanda hakan ya tilasta dole sai mutum ya yi tafiya mai nisa zuwa wasu ungu-wanni kafin ya samu kankara, kowace ake sayar da ledar Pure water daya kan 200. Sannan ga yanayin matsin rayuwa.”

A nashi bangaren kuma, Malam Abubakar Usman Damaturu, ya bayyana cewa rashin samun isasshen wutar lantarki a birnin shi ne ummul-haba’isan tsadar kankara tare da sauran kayan masarufi.

“Mafi yawan kankarar ana kawota ne daga Potiskum, wanda a farkon azumi kowace daya 500 ce (ba ta pure water ba). Sannan kuma zancen wutar lantarki kam sai dai mu ce Alhamdulillah.” In ji shi.

A Jihar Zamfara ma haka lamarin yake, domin kuwa al’ummar Jihar Zamfara al’umar na matukar shan wahala a wannan azumi wajen sanyaya makoshi a loka-cin buda baki.
Wannan ne ya sanya wasu su ka yi wa sana’ar sayar da kankara kutse ganin yad-da farashin ke hauhawa, musamman a Gusau babban birnin Jihar Zamfara.

Hamza Zurmi ya bayyana wa wakilinmu cewa, dafifi magidajan ke yi wajen sayan kakara ga layi mai tsawo duk da kuwa ba kowane yake samun yadda yake soba.

A yankin Janyau ta gabas da Samaru Gusau, a wani ashirin da hudu suke yi kan samun wuta lantarki, inda ake matukar shan wahala tare tsadar wajen sayen kankara.

Masu sayar da kankara a azumin bana sun yi camamarsu a mafi yawancin yankunan kasar nan sakamakon tsananin zafi da kuma rashin samun isasshin wutar lantarki.

Kankara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

Kisan Okuama: Baƙin Cikin Da Ke Tattare Da Labarin

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.