• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Taba Zabe A Nijeriya Mai Karancin Tashe-tashen Hankula Kamar Na 2023 Ba – Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa a tarihin Nijeriya ba a taba zabe mai karancin tashe-tashen hankula kamar na 2023 ba.

Ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed shi ya bayyana hakan a Birnin Washington a yayin ganawarsa da wasu cibiyoyin siyasa a babban birnin kasar Amurka.

  • Ohanaeze Ta Bukaci Tinubu Ya Saki Nnamdi Kanu Idan Aka Rantsar Da Shi

Ministan ya je Washington ne don yin tattaunawa da kafofin watsa labarai na kasa da kasa da cibiyoyin siyasa da sauransu, don samar da mafita ga kalubalen duniya.

Daga cikin wadanda ministan ya tattauna da su kan zaben 2023 da aka kammala sun hada da Cibiyar Hudson, Majalisar Atlantika da Cibiyar Wilson.

Dangane da bayanan da wata gamayyar kungiyoyin farar hula a Nijeriya ta fitar, Mohammed ya ce an samu rahoton mutuwar mutane tsakanin 13 zuwa 28 a zaben da aka kammala, shi ne mafi karanci tun bayan zaben 1964/65.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Mohammed ya ce a shekarar 1964/1965, a kalla mutane 200 ne suka mutu sakamakon rikicin zabe.
Ya ce zaben 1993, ya yi sanadiyar mutuwar mutane 100, a shekarar 1999 an samu mutuwar mutane 80, zaben 2003 ya yi sanadiyar mutuwar mutane 100, sannan an yi asarar rayuka 300 a zaben 2007.

A cewar ministan, zaben na 2011 ya yi sanadiyar mutuwar mutane 800, zaben 2015 ya yi sanadiyar mutuwar mutane 100, yayin da aka samu asarar rayuka 150 a zaben 2019.

Ministan ya jaddada muhimmacin rayuwa, inda ya bayyana cewa bai kamata dan Nijeriya ya rasa rans aba a lokacin zabe.Ya ce za a iya gudanar da zabe ba tare da rasa rai ba.

Mohammed ya ba da tabbacin cewa nan ba da dadewa ba kasar za ta kai ga matakin gudanar da zabukan kasa baki daya ba tare da an samu asarar rayuka ba.

Da yake mayar da martani ga kiraye-kirayen da ‘yan adawa suka yi na a soke zaben 2023, bisa zargin tashe-tashen hankula, ministan ya ce hakan babu adalci kuma abu ne wanda bai dace ba.

Ya ce ‘yansanda sun ba da rahoton tashe-tashen hankula da aka samu a ko’ina a kasar, amma ba su kai ga soke zaben ba.

Da yake magana kan rahoton ‘yansandan, ministan ya ce akwai kararraki 489 na laifukan zabe, sannan an kama mutum 781 da za a gurfanar da su a gaban kotu.

A cikin nazarin rahoton da ministan ya yi, ya ce an samu tashin hankali ne na kashi daya tak a sama da rumfunan zabe 300, wanda a cewarsa hakan bai wadatar ba a soke zaben.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ce-ce-ce-kucen Kafa Gwamnatin Rikon Kwarya: Dimbin Tambayoyin Da Aka Kasa Amsawa Har Yanzu

Next Post

Samar Da Matakan Kauce Wa Yunwa A Nijeriya

Related

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

9 minutes ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

9 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

11 hours ago
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

16 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

18 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

18 hours ago
Next Post
Yunwa

Samar Da Matakan Kauce Wa Yunwa A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.