• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba A Taba Zabe A Nijeriya Mai Karancin Tashe-tashen Hankula Kamar Na 2023 Ba – Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa a tarihin Nijeriya ba a taba zabe mai karancin tashe-tashen hankula kamar na 2023 ba.

Ministan yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed shi ya bayyana hakan a Birnin Washington a yayin ganawarsa da wasu cibiyoyin siyasa a babban birnin kasar Amurka.

  • Ohanaeze Ta Bukaci Tinubu Ya Saki Nnamdi Kanu Idan Aka Rantsar Da Shi

Ministan ya je Washington ne don yin tattaunawa da kafofin watsa labarai na kasa da kasa da cibiyoyin siyasa da sauransu, don samar da mafita ga kalubalen duniya.

Daga cikin wadanda ministan ya tattauna da su kan zaben 2023 da aka kammala sun hada da Cibiyar Hudson, Majalisar Atlantika da Cibiyar Wilson.

Dangane da bayanan da wata gamayyar kungiyoyin farar hula a Nijeriya ta fitar, Mohammed ya ce an samu rahoton mutuwar mutane tsakanin 13 zuwa 28 a zaben da aka kammala, shi ne mafi karanci tun bayan zaben 1964/65.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Mohammed ya ce a shekarar 1964/1965, a kalla mutane 200 ne suka mutu sakamakon rikicin zabe.
Ya ce zaben 1993, ya yi sanadiyar mutuwar mutane 100, a shekarar 1999 an samu mutuwar mutane 80, zaben 2003 ya yi sanadiyar mutuwar mutane 100, sannan an yi asarar rayuka 300 a zaben 2007.

A cewar ministan, zaben na 2011 ya yi sanadiyar mutuwar mutane 800, zaben 2015 ya yi sanadiyar mutuwar mutane 100, yayin da aka samu asarar rayuka 150 a zaben 2019.

Ministan ya jaddada muhimmacin rayuwa, inda ya bayyana cewa bai kamata dan Nijeriya ya rasa rans aba a lokacin zabe.Ya ce za a iya gudanar da zabe ba tare da rasa rai ba.

Mohammed ya ba da tabbacin cewa nan ba da dadewa ba kasar za ta kai ga matakin gudanar da zabukan kasa baki daya ba tare da an samu asarar rayuka ba.

Da yake mayar da martani ga kiraye-kirayen da ‘yan adawa suka yi na a soke zaben 2023, bisa zargin tashe-tashen hankula, ministan ya ce hakan babu adalci kuma abu ne wanda bai dace ba.

Ya ce ‘yansanda sun ba da rahoton tashe-tashen hankula da aka samu a ko’ina a kasar, amma ba su kai ga soke zaben ba.

Da yake magana kan rahoton ‘yansandan, ministan ya ce akwai kararraki 489 na laifukan zabe, sannan an kama mutum 781 da za a gurfanar da su a gaban kotu.

A cikin nazarin rahoton da ministan ya yi, ya ce an samu tashin hankali ne na kashi daya tak a sama da rumfunan zabe 300, wanda a cewarsa hakan bai wadatar ba a soke zaben.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ce-ce-ce-kucen Kafa Gwamnatin Rikon Kwarya: Dimbin Tambayoyin Da Aka Kasa Amsawa Har Yanzu

Next Post

Samar Da Matakan Kauce Wa Yunwa A Nijeriya

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

5 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

6 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

9 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

12 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

12 hours ago
Next Post
Yunwa

Samar Da Matakan Kauce Wa Yunwa A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.