• Leadership Hausa
Wednesday, December 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Samar Da Matakan Kauce Wa Yunwa A Nijeriya

by Abdulrazaq Yahuza
8 months ago
in Rahotonni
0
Yunwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bukukuwan da aka gudanar na ranar abinci na duniya kwanannan sun isa su jawo hankalin gwamnati da al’ummar kasashen duniya a kan matsalar abinci da ake fuskanta a Nijeriya dama wasu sassan duniya, wannan ya zama dole ne musamman ganin matsalar da aka fuskanta sakamakon annobar cutar Korona da kuma matsalar dumamar yanayi a duniya da kuma ambaliyar ruwar da aka fuskanta, ana wannan bikin ne a fadin duniya, ranar da ta yi daidai da ranar da aka kafa kungiyar nan ta Majalisar Dinkin Duniya ta UNFAO a shekarar 1945, bikin nada matukar muhimmanci don a wannan ranar ce al’ummar duniya ke haduwa don tattaunawa a kan matsalar da ake fuskanta na karancin abinci ko kuma rashin abinci gaba daya a wasu sassan duniya.

Kamar dai yadda shirin samar da abinci a duniya (WFP) ya sanar, shekarar 2022 ya zamar wa al’ummar duniya wata fage na fuskantar matsaloli da suka shafi yanayin samar da abinci wadanda suka hada da rikice-rikice kamar abin da ke faruwa a yakin Rasha da Yukrain da lamarin dumamar yanayi da hauhawar farashin kayan masarufi haka kuma tayar da jijiyar wuya a tsakanin kasashe yana kara haifar da yanayin da noma zai gagara wanda hakan zai ka gai haifar da matsalolin abinci. Wadannan matsalolin sun taimaka wajen haifar da rashin abinci irin wanda ba a taba gani ba a tarihi.

  • Sin Tana Son Ba Da Gudummawar Hikima Don Inganta Zaman Lafiya Da Ci Gaban Yankin Gabas Ta Tsakiya

Ra’ayin wannan jaridar ita ce, an dade ana ta surutu a kan bukatar samar da yanayi da al’umma duniya za su samu damar samun ingantaccen abinci mai gina jiki. A wannan mahangar muke jinjina da godiya da taken bikin na wannan shekarar wanda yake kamar haka, “Tafiya Tare Da Kowa Da Kowa Don Samar Da Ingantaccen Abinci Mai Gina Jiki.”

Taken na wannan shekarar ya nuna muhimmancin hadin kai a tsakanin al’ummar duniya don karfafa tsarin samar da abinci a fadin duniya gaba daya. Wannan ba tare da tantama ba suna cikin manyan matsalolin da al’umma duniya ke fuskanta, cikin su kuma akwai talauci, rashin lafiya da lalacewar muhalli. Don kawo karshen wannan matsalar a fadin duniya a ra’ayinmu dole a samar da wani tsari da zai tafi tare da dukkan al’umma ba tare da nuna banbanci ba domin ai dukkan al’ummar duniya na da muhimmanci wajen samun nasarar wannan aikin.
A kan haka dole Gwamnati, Kamfanoni masu zaman kansu da Malaman jami’o’i da kungiyoyi masu zaman kansu da sauran daidaikun mutane su yi aiki tare da don samar da yanayin da kowa zai samu abinci cikin kwanciyar hankali ba tare da wani mastala ba.

Abin takaici ne a ra’ayinmu, duk da kokarin da ake yi na samar da ingantacciyar al’umma har yanzu mutane da dama a baya ba a tafiya da su, sun kasa cin gajiyar cigaba da aka samu na kimiyya da fasaha a bangaren tattalin arziki dana zamantakewa. A bayyane lamarin yake, duniya nada abinci da al’umma duniya za su iya ci ba tare da matsala ba amma kuma miliyoyin mutane a fadin duniya na kwana da yunwa wasu kuma basu da ikon samun abinci mai gina jiki.

Labarai Masu Nasaba

Firimiyar Ingila: Man City Za Ta Karbi Bakuncin Liverpool A Etihad

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

Muna kara jaddada cewa, annobar cutar Korona, Dumamar yanayi da mamayar kasar Yukrain da Rasha ta yi ya kawo cikas ga kokarin samar da ingantaccen abinci ga al’umma duniya da kuma shirin kawar da yunwa a fadin duniya.

Kididdiga ya nuna cewa, kashi 75 na mutanen da suke fuskantar matsalar abinci mutane ne da suka dogara da harkar noma a matsayin hanyar samun abincin su, su ne kuma suka fi dandanawa sakamakon da annobar da dan adam ya haifar wa kansa yake kawowa, haka kuma sune suka fi fukantar rikice-rikicen da suka hada da na kabilanci da nuna banbanci a tsakanin maza da mata, wadannan mutanen na matukar bukatar tallafin kudade da kayan aikin noma na zamani don su samu hanyoyin samar da abinci ga al’ummarsu.

A daidai wannan rana ta abinci ta duniya, ya zama dole musamman ganin irin matsalolin da ake fuskanta a sassan duniya duniya su hada hannu don fuskantar matsalar ba tare da nuna banbanci ba, a kan haka dukkan bangarori na rayuwar al’umma suna da gudummawar da yakamata su bayar don samar da abinci ingantacce da zai samar wa al’umma cikakken lafiya.

Bincike ya nuna cewa, a shekafrar 2021 misali, an kiyasta cewa kashi 29.3 na al’ummar duniya kusan mutum Biliyan 2.3 na fuskantar tsanani ko tsakatsakanin matsalar abinci, haka kuma kashi 11.7 na al’umma duniya kusan mutum Biliyan 923.7 na fuskantar kololuwa tsananin matsalar abinci. Haka kuma banbancin da ake samu a tsakanin jinsin mata da maza a kan yadda suke samun abinci yana kara fadada a kullum. A shekarar 2021, kashi 31.9 na mata a duniya na fuskantar matsanancin rashin abinci in aka kwatanta da kashi 27.6 na maza. Rahoton ya kuma bayyana cewa a shekarar 2020, an kiyasta cewa kashi 22 na yara da basu gaza da shekara 5 suna fuskantar matsanancin rashin abinci, yayin da kashi 6.7 na yaran rashin abincin ya yi musu illa wasu kashi 5.7 na yaran kuma suna fuskantar cutar kiba saboda ciye ciye marasa kangado.

Rahoton ya kuma kiyasata cewa, fiye da mutum miliyan 670 a fadin duniya za su fuskanci rashin abinci a cikin shekarar 2030 zuwa 2038, haka lamarin yake a shekarar 2015 a lokacin da aka kaddamar da shirin samar da abinci ga al’ummar duniya nan da shekarar 2030. Mutum fiye da Miliyan 828 aka tabbatar sun fuskanci yunwa a shekarar 2021. Bincike ya kuma nuna cewa daya daga cikin magidanta 8 a duniya na fuskantar cutar kiba a kusan dukkan bangarorin duniya ciki har da kasashe masu tasowa.

Ga Nijeriya kuwa harkokin ‘yan ta’adda yana kara tayar da hankalin al’umma game da shirin samar da abinci sai kuma ga gaggarumar ambaliyar ruwar da ta share filayen noma masu yawa. Ra’ayinmu anan shi ne na bukatar gwamnati ta kawo dauki ga manoman da suka yi asara a sassan Nijeriya. Dole a gaggauta kawar da al’amarin da muke tsoron aukuwarsa.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba A Taba Zabe A Nijeriya Mai Karancin Tashe-tashen Hankula Kamar Na 2023 Ba – Gwamnatin Tarayya

Next Post

Zaben Jihar Zamfara: Zafin Kaye Ya Sa Gwamna Matawalle Sunbatu A Kan Sojoji

Related

Firimiyar Ingila: Man City Za Ta Karbi Bakuncin Liverpool A Etihad
Rahotonni

Firimiyar Ingila: Man City Za Ta Karbi Bakuncin Liverpool A Etihad

2 weeks ago
Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya
Rahotonni

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

2 weeks ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,127, Sun Sace 518 A Watan Oktoba – Rahoto
Rahotonni

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,127, Sun Sace 518 A Watan Oktoba – Rahoto

3 weeks ago
Abubuwan Da Ke Saurin Kashe Soyayya A Zuciyar Maigida
Rahotonni

Abubuwan Da Ke Saurin Kashe Soyayya A Zuciyar Maigida

1 month ago
Manyan Ayyukan Da Ke Gaban Sabon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya
Rahotonni

Tsarin Canji Na Bai-daya Hanya Ce Ta Tsaftace Kasuwar Shinku

1 month ago
Yadda NPA Ta Bunkasa Hanyoyin Tara Kudaden Shiga Da Inganta Fitar Da Kaya Waje
Rahotonni

Yadda NPA Ta Bunkasa Hanyoyin Tara Kudaden Shiga Da Inganta Fitar Da Kaya Waje

1 month ago
Next Post
Zaben Jihar Zamfara: Zafin Kaye Ya Sa Gwamna Matawalle Sunbatu A Kan Sojoji

Zaben Jihar Zamfara: Zafin Kaye Ya Sa Gwamna Matawalle Sunbatu A Kan Sojoji

LABARAI MASU NASABA

An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28

An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28

December 5, 2023
Taron COP28: Ba Sharholiya Ce Ta Kai Tinubu Da Tawagarsa Dubai ba – Ministan Yada Labarai 

Taron COP28: Ba Sharholiya Ce Ta Kai Tinubu Da Tawagarsa Dubai ba – Ministan Yada Labarai 

December 5, 2023
Kungiyar Jam’iyyatu Ansariddeen Attajjaniyya Ta Gindaya Sharudda 5 Bisa Kisan Masu Maulidi A Kaduna 

Kungiyar Jam’iyyatu Ansariddeen Attajjaniyya Ta Gindaya Sharudda 5 Bisa Kisan Masu Maulidi A Kaduna 

December 5, 2023
Sin Ta Sake Zama Memba A Rukunin A A Kungiyar IMO

Sin Ta Sake Zama Memba A Rukunin A A Kungiyar IMO

December 5, 2023
Wang Yi Ya Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na Tunawa Da Cika Shekaru 75 Da Wallafa Sanarwa Kan Hakkin Dan Adam Na Duniya

Wang Yi Ya Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na Tunawa Da Cika Shekaru 75 Da Wallafa Sanarwa Kan Hakkin Dan Adam Na Duniya

December 5, 2023
Kasar Sin: Yawan Kunshin Kayayyaki Da Aka Isar A Kasar Ya Kafa Wani Sabon Tarihi

Kasar Sin: Yawan Kunshin Kayayyaki Da Aka Isar A Kasar Ya Kafa Wani Sabon Tarihi

December 5, 2023
Sin Ta Yi Amfani Da Rokar CERES-1 Y9 Wajen Harba Sabbin Taurarin Dan Adam 

Sin Ta Yi Amfani Da Rokar CERES-1 Y9 Wajen Harba Sabbin Taurarin Dan Adam 

December 5, 2023
Babban Hafsan Sojin Kasa Ya Ziyarci Wurin Da Aka Kai Harin Bam A Kaduna Da Asibitin Da Ake Kula Da Masu Raunin

Babban Hafsan Sojin Kasa Ya Ziyarci Wurin Da Aka Kai Harin Bam A Kaduna Da Asibitin Da Ake Kula Da Masu Raunin

December 5, 2023
Jami’in Diflomasiyyar Falasdinu: PA Ta Godewa Kasar Sin Bisa Aikewa Da Agaji Ga ’Yan Gaza Cikin Sa’o’in Bukata

Jami’in Diflomasiyyar Falasdinu: PA Ta Godewa Kasar Sin Bisa Aikewa Da Agaji Ga ’Yan Gaza Cikin Sa’o’in Bukata

December 5, 2023
Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Bukaci A Gudanar Da Bincike Kan Kisan Masu Maulidi A Kaduna

December 5, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.